< John 6 >
1 After this Jesus went away across the Sea of Galilee (that is the lake of Tiberias).
Ɗan lokaci bayan wannan, sai Yesu ya ƙetare zuwa gaɓar mai nesa na Tekun Galili (wato, Tekun Tibariya),
2 A great crowd were following him, because they witnessed the signs which he was continually performing among those who were ill.
sai taro mai yawa na mutane suka bi shi domin sun ga abubuwan banmamakin da ya yi ga marasa lafiya.
3 Then Jesus walked up the hills and sat down there with his disciples. Now the Jewish feast, the Passover, was at hand.
Sa’an nan Yesu ya hau gefen dutse ya zauna tare da almajiransa.
4 Accordingly when he looked up, and perceived a great crowd was coming unto him,
Bikin Ƙetarewan Yahudawa ya yi kusa.
5 he said to Philip, "Where shall we buy bread for these people to eat?"
Sa’ad da Yesu ya ɗaga kai ya ga taro mai yawa suna zuwa wajensa, sai ya ce wa Filibus, “Ina za mu sayi burodi saboda mutanen nan su ci?”
6 He said this to test him, for he himself knew what he intended to do.
Ya yi wannan tambayar don yă gwada shi ne kawai, gama ya riga ya san abin da zai yi.
7 "Thirty-five dollars worth of bread," answered Philip, "is not enough for them, so that each can take a morsel."
Sai Filibus ya amsa ya ce, “Kai, ko albashin wata takwas ba zai iya sayan isashen burodin da kowa zai ɗan samu kaɗan ba!”
8 One of his disciples, Andrew, the brother of Simon, said to him.
Sai wani daga cikin almajiransa Andarawus, ɗan’uwan Bitrus, ya yi magana,
9 "There is a lad who has five barley loaves and a couple of fish; but what is that among so many?"
“Ga wani yaro da ƙananan burodin sha’ir guda biyar da ƙananan kifi biyu, amma me wannan zai yi wa yawan mutanen nan.”
10 "Make the men sit down," said Jesus. The ground was covered with thick grass; so the men sat down, in numbers about five thousand. "of righteousness, because I am going to my Father, and you will no longer see me;
Yesu ya ce, “Ku sa mutanen su zauna.” Wurin kuwa akwai ciyawa da sosai, sai maza suka zazzauna, sun kai wajen dubu biyar.
11 Then Jesus took the loaves, and when he had given thanks he distributed them among those who were seated; in like manner also of the fish, as much as they wished,
Sa’an nan Yesu ya ɗauki burodin, ya yi godiya, ya kuma rarraba wa waɗanda suke zaune gwargwadon abin da ya ishe su. Haka kuma ya yi da kifin.
12 and when they were satisfied, he said to his disciples, "Gather up the fragments that are left, so that nothing may be wasted."
Sa’ad da duk suka ci suka ƙoshi, sai ya ce wa almajiransa, “Ku tattara gutsattsarin da suka rage. Kada kome yă lalace.”
13 So they gathered them up, and filled twelve baskets with the fragments of the five barley loaves - the broken pieces that were left after they had eaten.
Saboda haka suka tattara su suka kuma cika kwanduna goma sha biyu na gutsattsarin burodin sha’ir biyar nan da suka ragu bayan kowa ya ci.
14 So when the people saw the sign which he had performed, they said, "This is in the truth the Prophet who is to come into the world."
Bayan mutanen suka ga abin banmamakin da Yesu ya yi, sai suka fara cewa, “Lalle, wannan shi ne Annabin nan mai zuwa duniya.”
15 When Jesus perceived that they intended to seize him in order to make him a king, he retired again to the hill all by himself.
Da Yesu ya gane suna shirin su ɗauke shi ƙarfi da yaji su naɗa shi sarki, sai ya sāke komawa kan dutsen shi kaɗai.
16 When evening came on, his disciples went down to the sea.
Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara zuwa tafki,
17 There they got in a boat, and started across the sea for Capernaum. The darkness had already fallen,
inda suka shiga jirgin ruwa suka tasar wa haye tafkin zuwa Kafarnahum. A lokacin kuwa duhu ya yi, Yesu kuma bai riga ya zo wurinsu ba tukuna.
18 Jesus had not yet come to them, and the sea began to rise, because a strong wind was blowing.
Iska mai ƙarfi kuwa tana bugowa, ruwaye kuma suka fara hauka.
19 After they had rowed three or four miles, they saw Jesus walking upon the sea, and drawing near to the boat, and they were terrified;
Bayan sun yi tuƙi wajen mil uku ko uku da rabi, sai suka ga Yesu ya kusato jirgin ruwan, yana takawa a kan ruwan; sai suka tsorata.
20 but he said to them, "It is I, be not afraid."
Amma ya ce musu, “Ni ne; kada ku ji tsoro.”
21 Then they were willing to take him on board, and immediately the boat reached the shore they were making for.
Sa’an nan suka yarda suka karɓe shi a cikin jirgin ruwan, nan da nan kuwa jirgin ya kai gaɓar da za su.
22 The crowd that remained on the other side of the sea had seen that there was only one small boat there, and that Jesus had not gone aboard with his disciples, but that his disciples had gone away by themselves.
Kashegari taron da suka tsaya a wancan ƙetaren tafkin suka lura cewa jirgin ruwa ɗaya ne yake a can dā ma, kuma sun lura cewa Yesu bai shiga ciki tare da almajiransa ba, gama sun tashi su kaɗai.
23 So, on the following day, when boats came from Tiberias near the place were they had eaten bread, after the Lord had given thanks, they got into the boats themselves,
Sai ga waɗansu jiragen ruwa daga Tibariya suka iso kusa da wurin da mutanen suka ci burodi bayan Ubangiji ya yi godiya.
24 when they saw that neither Jesus nor his disciples were there, and went to Capernaum to look for Jesus.
Da taron suka lura cewa Yesu da almajiransa ba sa can, sai suka shiga jiragen ruwa suka tafi Kafarnahum neman Yesu.
25 When they found him on the other side of the sea, they said to him, "Rabbi, when did you get here?"
Da suka same shi a wancan ƙetaren tafkin, sai suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, yaushe ka kai nan?”
26 Jesus answered. "In solemn truth I tell you that you are looking for me, not because you saw miracles signs, but because you ate of the bread and were filled.
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, kuna nemana ne ba don kun ga abubuwan banmamaki ba, sai dai domin kun ci burodi kun ƙoshi.
27 "Labor not for food which perishes, but for the food that endures eternal life - that which the Son of man will give you; for on the Father - God - has set his seal." (aiōnios )
Kada ku yi aiki saboda abincin da yake lalacewa, sai dai saboda abinci mai dawwama har yă zuwa rai madawwami, wanda Ɗan Mutum zai ba ku. A kansa ne Allah Uba ya sa hatimin amincewarsa.” (aiōnios )
28 "What are we to do habitually," they asked him, "that we may keep working the words of God?"
Sai suka tambaye shi suka ce, “Me za mu yi don mu aikata ayyukan da Allah yake so?”
29 "This is the work of God," answered Jesus, "that you believe on him whom He has sent you."
Yesu ya amsa, “Aikin Allah shi ne, a gaskata da wanda ya aiko.”
30 The they said to him. "What sign, then, are you performing, so that we may see it and believe in you? What work are you doing?
Sai suka tambaye shi, “Wace abin banmamaki ce za ka yi don mu gani mu kuwa gaskata ka? Me za ka yi?
31 "Our fathers ate manna in the wilderness, as it is written, ‘He gave them bread out of heaven to eat.’"
Kakannin-kakanninmu sun ci Manna a hamada; kamar yadda yake a rubuce, ‘Ya ba su burodi daga sama su ci.’”
32 "In solemn truth I tell you," said Jesus in reply, "Moses did not give you the bread out of heaven, but my Father does give you the true bread out of heaven;
Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba Musa ne ya ba ku burodi daga sama ba, sai dai Ubana ne yake ba ku burodi na gaskiya daga sama.
33 "for the bread of God is what come down from heaven, and gives life to the world."
Gama burodin Allah shi ne wanda yake saukowa daga sama, yana kuma ba wa duniya rai.”
34 "Ah, Sir," said they, "evermore give us this bread."
Sai suka ce, “Ranka yă daɗe, daga yanzu ka dinga ba mu wannan burodi.”
35 "I myself am the bread of life," answered Jesus; "he who comes to me shall never hunger, and he that believes on me shall never thirst again.
Sa’an nan Yesu ya furta cewa, “Ni ne burodin rai. Wanda ya zo wurina ba zai taɓa jin yunwa ba, wanda kuma ya gaskata da ni ba zai taɓa jin ƙishirwa ba.
36 "But as I told you, you have seen me, and yet you do not believe.
Amma kamar yadda na faɗa muku, kun gan ni duk da haka ba ku gaskata ba.
37 "Everyone whom the Father gives me will come to me; and him who comes to me I will never reject.
Duk waɗanda Uba ya ba ni za su zo wurina, kuma duk wanda ya zo wurina ba zan kore shi ba ko kaɗan.
38 "For I am come down from heaven, not to do my own will, but the will of him who sent me.
Gama na sauko daga sama ba don in cika nufin kaina ba sai dai don in cika nufin shi wanda ya aiko ni.
39 "And this is the will of him who sent me, that I should not lose one of all those whom he has given me, but should raise them up at the last day.
Nufin wanda ya aiko ni kuwa shi ne, kada in yar da ko ɗaya daga cikin duk waɗanda ya ba ni, sai dai in tashe su a rana ta ƙarshe.
40 "For this is my Fathers will, that every one who beholds the Son and believes on him, shall have eternal life. and I will raise him up at the last day." (aiōnios )
Gama nufin Ubana shi ne, duk wanda yake duban Ɗan, ya kuma gaskata shi zai sami rai madawwami, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.” (aiōnios )
41 Then the Jews began to find fault with Jesus, because he said, "I am the bread which comes down out of heaven," and they kept asking.
Da jin haka, Yahudawa suka fara gunaguni a kansa, domin ya ce, “Ni ne burodin da ya sauka daga sama.”
42 "Is not this Jesus, the son of Joseph? Do we not know his father and mother? How is it that he now says, ‘I have come down from heaven’?"
Suka ce, “Kai, wannan ba Yesu ba ne, ɗan Yusuf, wanda mahaifinsa da mahaifiyarsa duk mun san su? Yaya yanzu zai ce, ‘Na sauko daga sama?’”
43 "Do not find fault with me among yourselves,"
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ku daina gunaguni a junanku.
44 answered Jesus; "no one can come to me unless the Father who sent me draw him; then I will raise him up on the last day.
Ba mai iya zuwa wurina, sai dai in Uban da ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.
45 "It is written in the Prophets, "And they shall all of them be taught of God. Every one who has listened to the father and learns from him, comes to me.
A rubuce yake a cikin Annabawa cewa, ‘Allah zai koyar da dukansu.’Duk wanda ya saurari Uba, ya kuma koyi daga wurinsa, zai zo wurina.
46 "Not that any one has seen the Father, except the one who is from God; he has seen the Father.
Ba wanda ya taɓa ganin Uban, sai shi wanda ya zo daga Allah; shi ne kaɗai ya taɓa ganin Uban.
47 "I tell you solemnly that he who believes has eternal life. (aiōnios )
Gaskiya nake gaya muku, wanda ya gaskata yana da rai madawwami. (aiōnios )
48 "I am the bread of life.
Ni ne burodin rai.
49 "Your fathers ate the manna in the wilderness; yet they died.
Kakannin-kakanninku sun ci Manna a hamada, duk da haka suka mutu.
50 "This is the bread that comes down from heaven, that one may eat thereof and never die.
Amma ga burodin da ya sauko daga sama, wanda mutum zai iya ci, ba zai kuma mutu ba.
51 "I myself am the living bread that has come down from heaven. Any one who eats this bread will live forever; and moreover, the bread which I will give is my flesh, given for the life of the world." (aiōn )
Ni ne burodin rai mai saukowa daga sama. Duk wanda ya ci wannan burodi, zai rayu har abada. Wannan burodin shi ne jikina, da zan bayar don duniya ta sami rai.” (aiōn )
52 Then the Jews began to dispute among themselves, saying, "How can this man give us his flesh to eat?"
Sai Yahudawa suka fara gardama mai tsanani a junansu suna cewa, “Yaya wannan mutum zai ba mu naman jikinsa mu ci?”
53 "I tell you solemnly," said Jesus, "that unless you eat the flesh of the Son of man, and drink his blood, you have no life in you.
Sai Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, sai kun ci naman jikin Ɗan Mutum kuka kuma sha jininsa, ba za ku kasance da rai a cikinku ba.
54 "He who feeds upon my flesh and drinks my blood has eternal life, and I will raise him up on the last day. (aiōnios )
Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana da rai madawwami. Ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe. (aiōnios )
55 "For my flesh is true food, and my blood is true drink.
Gama naman jikina abinci ne na gaskiya jinina kuma abin sha ne na gaskiya.
56 "He who feeds upon my flesh abides in me and I in him.
Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana cikina, ni kuma ina cikinsa.
57 "Just as the living Father has sent me, and I live by the Father, so also that man who feeds on me shall live by me.
Kamar dai yadda Uba mai rai ya aiko ni, ina kuma rayuwa ta saboda shi, haka ma wanda yake ni ne abincinsa zai rayu saboda ni.
58 "This is the bread which came down from heaven; not such as your fathers ate and died, for he who feeds upon this bread shall live forever." (aiōn )
Wannan shi ne burodin da ya sauko daga sama. Kakannin-kakanninku sun ci Manna suka kuma mutu, amma duk wanda yake cin wannan burodi zai rayu har abada.” (aiōn )
59 He spoke these words while in the synagogue, while he was teaching in Capernaum.
Ya faɗi wannan ne lokacin da yake koyarwa a cikin majami’a a Kafarnahum.
60 So many of his disciples, when they heard it, said. "This teaching is unbelievable! Who can listen to him?"
Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan koyarwa tana da wuya. Wa zai iya yarda da ita?”
61 Jesus, conscious within himself that his disciples were finding fault with him about his teaching, said to them.
Da yake ya san almajiransa suna gunaguni game da wannan, sai Yesu ya ce musu, “Wannan ya ɓata muku rai ne?
62 "Does this displease you? What then if you were to behold the Son of man ascending to where he was before?
Me za ku ce ke nan, in kuka gan Ɗan Mutum yana hawa zuwa inda yake dā!
63 "The spirit is what gives life; the flesh is of no avail. The words which I have been speaking to you, are spirit and are life.
Ruhu ne yake ba da rai; jikin kam, ba ya amfana kome. Kalmomin da na faɗa muku, Ruhu ne, da kuma rai.
64 "Yet there are some of you who do not believe." For Jesus knew from the beginning who they were who did not believe, and who it was who should betray him.
Duk da haka akwai waɗansunku da ba su gaskata ba.” Gama Yesu ya sani tun farko, waɗanda ba su gaskata ba, da kuma wanda zai bashe shi.
65 So he added, "This is why I told you that no on can come to me unless it be given from the Father."
Ya ci gaba da cewa, “Shi ya sa na faɗa muku cewa ba mai iya zuwa wurina, sai dai Uba ya yardar masa.”
66 Therefore many of his disciples drew back and no longer companied with him.
Daga wannan lokaci da yawa daga cikin almajiransa suka ja da baya, suka daina bin sa.
67 So Jesus appealed to the Twelve. "You also do not wish to leave me, do you?"
Sai Yesu ya tambayi Sha Biyun, “Ku ma za ku tafi ne?”
68 Simon Peter answered. "To whom shall we go Master? You have words of eternal life; (aiōnios )
Sai Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji wajen wa za mu tafi? Kai ne da kalmomin rai madawwami. (aiōnios )
69 "and we have learned to believe and we know that you are the holy one of God."
Mun gaskata mun kuma san cewa kai ne Mai Tsarkin nan na Allah.”
70 In reply Jesus said to them. "Have I not chosen you, the Twelve? And yet even of you one is an enemy."
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ba ni na zaɓe ku Sha Biyu ba? Amma ɗayanku Iblis ne!”
71 Now Jesus was speaking of Judas, the son of Simon Iscariot; for Judas was to betray him, although he was one of the Twelve.
(Yana nufin Yahuda, ɗan Siman Iskariyot, wanda, ko da yake ɗaya ne cikin Sha Biyun, zai bashe shi daga baya.)