< Romans 10 >

1 Brethren, indeed my heart's desire and prayer to God for them, is, that they may be saved.
'Yan'uwana, muradin zuciyata da dukkan addu'oi na ga Allah dominsu shine don su sami ceton.
2 For I testify to God for them, that they have a zeal for God; but not according to knowledge;
Domin na shaida game da su cewa suna da kwazo game da Allah, amma ba a kan sani ba.
3 for being ignorant of God's justification, and seeking to establish their own, they have not submitted to the justification which is of God.
Don, ba su da sani akan adalcin Allah, suna kokarin tabbatar da adalcin kansu. Ba su bada kan su ga adalcin Allah ba.
4 For Christ is the end of the law for justification to every believer.
Gama Almasihu shi ne cikar doka zuwa ga adalci ga dukkan wadanda suka gaskata.
5 Now Moses describes the justification which is by the law, that "the man who does these things shall live by them."
Musa kam ya rubuta game da adalci da zai samu ta shari'a: ''mutumin da ya aikata adalcin shari'a, zai rayu ta wurin wannan adalcin.''
6 But the justification which is by faith speaks thus: Say not in your heart, Who shall ascend into heaven? that is, to bring Christ down.
Amma adalcin da ya zo ta wurin bangaskiya yace, ''Kada ku ce a zuciyarku, wa zai hau zuwa sama?''(don ya sauko da Almasihu kasa).
7 Or, Who shall descend into the abyss? that is, to bring up Christ from the dead. (Abyssos g12)
Kada ku ce, ''Wa zai gangara zuwa kasa?'' (Wato wa zai fito da Almasihu daga cikin matattu). (Abyssos g12)
8 But what does it say? (The word is near you--in your mouth, and in your heart; that is, the word of faith which we preach: )
Amma me yake cewa? “kalmar tana kusa da kai a cikin bakinka da kuma cikin zuciyarka.” Wato kalmar bangaskiya, wadda muke shaidawa.
9 that if you will openly confess with your mouth, that Jesus is Lord, and believe with your heart that God raised him from the dead, you shall be saved.
Don idan da bakinka, ka shaida Yesu Ubangiji ne, kuma ka gaskata a zuciyarka cewa Allah ya tashe shi daga matattu, za ka sami ceto.
10 (For with your heart man believes to justification: and with your mouth confession is made to salvation.)
Don da zuciya ne mutum yake gaskatawa zuwa ga adalci, da kuma baki ne yake shaida zuwa ga ceto.
11 For the scripture says, "No one, who believes on him, shall be ashamed."
Don nassi na cewa, ''Duk wanda ya gaskata da shi ba zai ji kunya ba,''
12 Indeed, there is no distinction either of Jew or of Greek: for the same Lord of all, is right toward all who call upon him.
Gama ba bambanci tsakanin Bayahude da Ba'al'ume. Gama dukkansu Ubangijinsu daya ne, Shi mayalwaci ne ga dukkan wanda ya kira shi.
13 "For whoever will call on the name of the Lord shall be saved."
Duk wanda ya kira sunan Ubangiji zai sami ceto.
14 But how shall they call on him in whom they have not believed? and how shall they believe in him, of whom they have not heard? and how shall they hear, without a proclaimer?
To ta yaya zasu kira ga wanda basu gaskata ba? Kuma ta yaya zasu gaskata ga wanda ba su taba jin labarinsa ba?
15 and how shall proclaim, unless they be sent? as it is written, "How beautiful are the feet of them, who bring the joyful message of peace--of them, who bring the joyful news of good things!"
Kuma ta yaya zasu ji in ba ayi masu wa'azi ba? Kuma ta yaya zasu yi wa'azin in ba an aike su ba? - Kamar yadda yake a rubuce, “Ina misalin kyau na kafafun wadanda ke shaida labarin farin ciki na abubuwa masu kyau!”
16 Nevertheless, all have not obeyed the gospel; for Isaiah says, "Lord, who has believed our report?"
Amma ba dukkansu ne suka ji bishara ba. Gama Ishaya ya ce, ''Ubangiji, wa ya gaskata da sakon?
17 (So, then, faith comes by hearing, and hearing by the word of God.)
Saboda haka bangaskiya na zuwa ta wurin ji, jin kuwa daga maganar Almasihu.
18 But I ask, have they not heard? Yes, indeed, "Their sound has gone out to all the earth, and their words to the ends of the world."
Amma na ce, “ko basu ji ba ne? I, tabbas'' muryarsu ta kai dukkan duniya, kuma kalmominsu sun kai har karshen duniya.''
19 I ask again, has not Israel known? First, Moses says, "I will provoke you to jealousy by that, which is no nation; --by a foolish nation I will enrage you."
yau, na ce, ''Ko Isra'ila basu sani ba ne?'' Da farko Musa ya ce, “Zan sa kuyi fushi da kishi da abin da ba al'umma ba. Abin da nake nufi nan shine al'ummar da basu da fahinta, zan more su, in tayar maku da hankali.''
20 Besides, Isaiah is very bold when he says, "I am found by them, who did not seek me: I am shown to them, who did not ask for me."
Amma Ishaya da karfin hali ya ce, ''Ga wadanda basu neme ni ba suka same ni. Na bayyana ga wadanda basu nemi ni ba.
21 But concerning Israel he says, "All the day long, have I stretched forth my hand to a disobedient and rebelling people."
''Amma ga Isra'ila kam ya ce, '' na mika hannu na ga masu rashin biyayya dukkan tsawon rana, domin su mutane ne masu taurin kai.''

< Romans 10 >