< Revelation 6 >

1 And I saw, when the Lamb opened one of the seals; and I heard one of the four living creatures, which said, as with a voice of thunder, Come and see.
Na duba lokacin da Dan Ragon ya bude daya daga cikin hatiman bakwai, sai na ji daya daga cikin rayayyun halittattun hudu ya fada da murya kamar tsawa, ''Zo!”
2 And I saw, and behold, a white horse; and he who sat upon it, had a bow, and there was given him a crown; and he went forth conquering, and to conquer.
Sai Na duba sai ga wani farin doki, mahayinsa na rike da baka, kuma an bashi rawani. Ya fito a matsayin mai nasara domin ya yi nasara.
3 And when he opened the second seal, I heard the second living creature, saying, Come--
Sa'anda Dan Ragon ya bude hatimi na biyu, sai na ji rayayyen halitta na biyu ya ce, ''Zo!''
4 And another horse came out, which was red; and it was given to him who sat upon it, to take peace from the earth, and that they should slay each other; and there was given to him a great sword.
Sai wani doki ya fito waje - jawur. Ga mahayin aka bashi dama ya dauke salama daga duniya, domin mutanen ta su karkashe juna. Wannan mahayin an bashi babbar takobi.
5 And when he had opened the third seal, I heard the third living creature, saying, Come and see. And I saw, and behold, a black horse; and he who sat upon it, has a pair of scales in his hand.
Sa'anda Dan Ragon ya bude hatimi na uku, sai na ji rayayyen halita na uku ya ce, ''Zo!'' Na ga bakin doki, mai hawanta na rike da ma'auni a cikin hannunsa.
6 And I heard a voice in the midst of the four living creatures, saying, A chenix of wheat for a denarius, and three chenices of barley for a denarius; you see that you injure not the oil, nor the wine.
Sai na ji kamar wata murya daga cikin rayayyun halittattun nan hudu ta ce, “Mudun alkama guda a kan albashin yini, kuma mudun sha'ir uku. Amma kar ka bata mai da kuma ruwan inabi.”
7 And when he opened the fourth seal, I heard the voice of the fourth living creature, saying, Come and see.
Da Dan Ragon ya bude hatimi na hudu, na ji muryar rayayyen halitta na hudu ya ce, ''Zo!''
8 And I saw, and behold, a pale horse; and as for him who sat on it, his name was Death; and Hades followed him: and there was given to him power to slay the fourth part of the earth with the sword, and with famine, and with death, and with the wild beasts of the field. (Hadēs g86)
Sai na ga wani doki ruwan toka. Mai hawansa an bashi suna mutuwa, hades kuma tana biye da shi. An basu iko bisa kashi hudu na duniya su kashe da takobi, yunwa, cututtuka, da kuma namomin jeji na duniya. (Hadēs g86)
9 And when he opened the fifth sea, I saw, under the altar, the souls of those who were slaughtered on account of the word of God, and the testimony which they held.
Da Dan Ragon ya bude hatimi na biyar, a karkashin bagadi sai na ga rayukan wadanda aka kashe saboda maganar Allah, da kuma shaidar da suka rike.
10 And they cried with a loud voice, and said, How long, O sovereign Lord, holy and true, before thou dost judge, and avenge our blood upon those who dwell on the earth?
Suka yi kuka da babban murya, ''Sai yaushe ya mai iko duka, Mai Tsarki da gaskiya, zaka shari'anta mazaunan duniya, ka kuma dauki fansar jininmu?
11 And there were given to each of them white robes; and it was said to them, that they should rest yet a while, till the number of their fellow-servants and brethren who should be killed, as they had been, should be completed.
Sai kowanne dayan su aka bashi farar tufa aka kuma fada masu su kara jira na lokaci kadan har sai adadin abokan bautar su da kuma 'yan'uwansu maza da mata wadanda aka kashe ya cika, kamar yadda aka kashe su.
12 And I saw, when he opened the sixth seal, and there was an earthquake; and the sun became black as sackcloth of hair; and the moon became as blood;
Da Dan Ragon ya bude hatimi na shidan, ina kallo sai ga babbar girgizar kasa. Rana ta zama baki kirin kamar bakar tufa, wata kuma ya zama kamar jini.
13 and the stars fell from heaven, on the earth, as fig tree drops its untimely figs, being shaken by a mighty wind:
Taurarin sama suka fado kasa, kamar yadda itacen baure ke karkade 'ya'yansa da basu nuna ba, yayin da babbar iska ta kada.
14 and the heavens passed away like a scroll, when it is rolled up; and every mountain, and island, was moved out of its place:
Sama kuma ta bace kamar takardar da aka nannade. Kowanne dutse da tsibiri aka kau da shi daga wurinsa.
15 and the kings of the earth, and the grandees, and the rich men, and the chief officers, and the powerful men, and every slave, and every freeman, hid themselves in the caves, and rocks of the mountains:
Sai sarakan duniya da muhimman mutane da sarakunan yaki, attajirai, da masu iko, tare da kowanne mutum, bawa da 'yantacce suka boye cikin duwatsu da tsaunuka.
16 and they said to the mountains, and the rocks, Fall on us, and hide us from the face of him who sits on the throne, and from the wrath of the Lamb!
Suka ce wa tsaunuka da duwatsu, “Ku fado bisan mu! Ku boye mu daga fuskar wanda yake zaune bisa kursiyin da kuma fushin Dan Ragon.
17 for the great day of his wrath is come, and who shall be able to stand?
Domin babban ranar fushin sa ta zo. Wa zai iya tsayawa?''

< Revelation 6 >