< Revelation 16 >
1 And I heard a great voice out of the temple saying, to the seven angels, Go, and pour out the vials of the wrath of God upon the earth.
Na ji babban murya na kira daga cikin haikali tana ce wa malai'iku bakwai, ''Ku je ku zuba tasoshi bakwai na fushin Allah a kan duniya.”
2 And the first went forth, and poured out his vial upon the earth; and there was a malignant and grievous ulcer upon the men who had the mark of the beast, and upon them who worshiped his image.
Mala'ika na fari ya je ya zuba tasarsa a kan duniya; munanan gyambuna masu zafi suka fito wa mutane wadanda suke da alamar dabbar, wadanda suka bauta wa siffarsa.
3 And the second angel poured out his vial upon the sea; and it became blood, like that of a dead man: and every living soul that was in the sea died.
Mala'ika na biyu ya zuba tasarsa cikin teku. Ya zama jini, kamar jinin wanda ya mutu, kuma kowane abu mai rai da ke cikin tekun ya mutu.'
4 And the third angel poured out his vial upon the rivers, and on the fountains of water; and they became blood.
Malaika na uku ya zuba tasarsa a cikin rafuffuka da mabulbulan ruwa, sai suka zama jini.
5 And I heard the angel of the waters saying, Righteous art thou, who art, and who wast; who art perfect; because thou hast judged these:
Na ji mala'ikan ruwaye ya ce, ''Kai mai adalci ne - wanda ya ke yanzu wanda yake kuma a da, Mai Tsarkin nan, domin ka shari'anta wadannan abubuwa.
6 for they have poured forth the blood of saints, and prophets; and thou hast given them blood to drink--they are worthy.
Domin sun zubar da jinin masu ba da gaskiya da annabawa, ka basu jini su sha; shine abinda da ya dace da su.
7 And I heard a voice from the altar, saying, Yes, O Lord God Almighty, true and righteous are thy judgments.
Na ji bagadi ya amsa, ''I, Ubangiji Allah Mai iko duka, shari'un ka gaskiya ne da adalci.''
8 And the fourth angel poured forth his vial on the sun; and power was given to it to scorch men with fire.
Mala'ika na hudu ya zuba tasarsa a kan rana, kuma aka ba shi izini ya kone jama'a da wuta.
9 And men were scorched with great heat, and they reviled the name of God, who had power over these plagues, and reformed not, to give him glory.
Suka kone da zafi mai tsanani, kuma suka sabi sunan Allah, wanda ke da iko akan annobai. Ba su tuba ba ko su daukaka shi.
10 And the fifth poured forth his vial upon the throne of the beast; and his kingdom was darkened, and they gnawed their tongues for
Sai malaika na biyar ya zuba tasarsa a kan kursiyin dabban, sai duhu ya rufe mulkinsa. Suka cicciji harsunansu saboda zafi.
11 anguish, and reviled the God of heaven for their pains and their ulcers, and reformed not from their works.
Suka yi sabon Allah na sama domin zafi da gyambunansu, suka kuma ki su tuba daga abin da suka yi.
12 And the sixth poured forth his vial upon the great river Euphrates; and its water was dried up, that a way might be prepared for the kings from the rising of the sun.
Mala'ika na shida ya zuba tasarsa cikin babban rafi, Yufiretis. Ruwansa ya bushe domin a shirya hanya da sarakuna za su zo daga gabas.
13 And I saw, and out of the mouth of the dragon, and out of the mouth of the beast, and out of the mouth of the false prophet there came forth three unclean spirits, like frogs:
Na ga kazamun ruhohi uku suna kama da kwadin da ke fitowa daga bakin diragon, da makaryacin annabi.
14 for these are the spirits of demons, working miracles, which go forth to the kings of the whole world, to bring them together to the battle of that great day of God Almighty.
Gama su ruhohin aljanu ne masu aikata alamun ban mamaki. Sun fita za su wurin sarakunan dukan duniya domin su tattaro su wuri daya saboda yaki a babbar ranar Allah Mai iko duka.
15 Behold, I come as a thief. Blessed is he that watches, and keeps his garments, that he may not walk naked, so that they should see his shame.
(''Duba! Ina zuwa kamar barawo! Mai albarka ne wanda ke zaune a fadake, wanda ke sanye da tufafinsa domin ba zai fita tsirara a ga tsiraicin sa ba.”)
16 And he gathered them together into a place which is called, in the Hebrew language, Armageddon.
Aka kawo su tare a wurin da ake kira Armagiddon da Ibraniyanci.
17 And the seven poured forth his vial into the air; and there came forth a great voice from the temple of heaven, from the throne, saying, It is done.
Mala'ika na bakwai ya zuba tasarsa cikin iska. Sa'annan babbar murya ta fito daga cikin haikali da kuma kursiyin, cewa, ''An gama!''
18 And there were voices, and thunders, and lightnings; and there was a great earthquake, such as there had not been from the time that men were upon the earth; such and so great an earthquake.
Aka yi walkiya, da kararraki masu tsanani, da aradu da babbar girgizar kasa - girgizar da ta fi kowacce da aka taba yi tun da 'yan adam suke a duniya, girgizar da girma ta ke.
19 And the great city was divided into three parts, and the cities of the Gentiles fell down. And Babylon the great came into remembrance before God, to give her the cup of the wine of his fiercest wrath.
Babban birnin ya rabu kashi uku, kuma biranen al'ummai suka fadi. Sai Allah ya tuna da Babila mai girma, sai ya ba wancan birnin koko cike da ruwan innabi wanda aka yi daga fushinsa mai tsanani.
20 And every island fled away, and the mountains were found no more.
Kowanne tsibiri ya bace, sai ba a kara ganin duwatsun ba.
21 And a great hail, as of the weight of a talent, descended from heaven upon men: and men reviled God, because of the plague of the hail; for the plague of it was very great.
Manyan duwatsun kankara, masu nauyin talanti, suka fado daga sama kan mutane. Suka zagi Allah domin annobar kankarar saboda annobar ta yi tsanani.