< Matthew 20 >
1 For the Administration of Heaven will resemble the conduct of a householder, who went out early in the morning to hire laborers for his vineyard.
Gama mulkin sama yana kama da wani mai gona, wanda ya fita da asuba ya nemi 'yan kwadago da za su yi aiki a gonarsa.
2 Having agreed with some for a denarius a-day, he sent them into his vineyard.
Bayan sun shirya kudin da zai biya ma'aikata kimanin dinari daya a kowanne yini, sai ya aike su gonarsa suyi aiki.
3 About the third hour he went out, and seeing others unemployed in the market place,
Misalin sa'a ta uku sai ya sake fita, sai ya ga wasu ma'aikata suna tsaye a bakin kasuwa, babu aiki.
4 said to them, Go you likewise into my vineyard, and I will give you what is reasonable. Accordingly they went.
Sai ya ce masu, 'Kuzo kuyi aiki a gonar, duk abinda ya wajaba, zan ba ku,' Sai suka tafi su yi aikin.
5 Again, about the sixth hour, and about the ninth, he went out and did the same.
Sai ya sake fita a sa'a ta shida ya kuma sake fita a sa'a ta tara, ya sake yin hakan din.
6 Lastly, about the eleventh hour, he went out, and finding others standing, said to them, Why do you stand here all the day doing nothing?
Ya kuma sake yin haka a sa'a ta sha daya, da ya fita sai ya ga wasu a tsaye da ba sa yin kome. Sai ya ce masu, 'Me yasa kuke tsaye ba ku yin kome dukan yini?'
7 They answered, Because no person has hired us. He said to them, Go you also into my vineyard, and you shall receive what is reasonable.
Sai suka ce masa, 'Ai babu wanda ya dauke mu aiki, shi yasa.' Sai ya ce masu, 'ku ma, kuje cikin gonar.
8 When it was night, the proprietor of the vineyard said to his steward, Call the laborers, and pay them their wages, beginning with the last, and ending with the first.
Da yamma ta yi, sai mai gonar ya ce wa manajansa, 'Ka kira ma'aikatan nan ka biya su hakkin su, amma ka fara da wadanda suka zo a karshe, zuwa na farkon.'
9 Then they who had been hired at the eleventh hour came, and received each a denarius.
Sa'adda wadanda suka fara aiki da yamma suka zo, an biya su daidai yadda ake biya a yini.
10 When the first came, they imagined they should receive more; but they got only a denarius a-piece.
Da wadanda suka fara aiki tun safe suka zo, suna tsammani za a ba su fiye da wadanda sun zo daga baya, amma aka ba kowannensu dinari daya.
11 Upon receiving it, they murmured against the householder,
Da suka karbi hakkinsu, suka yi gunaguni game da mai gonar.
12 saying, These last have worked but one hour; yet you have made them equal to us, who have borne the burden and heat of the day.
Suka ce, 'Wadannan da suka zo a karshe, sa'a guda ce kadai suka yi aiki, amma ka ba su daidai da mu, mu da muka yi fama da aiki cikin zafin rana.'
13 He answering, said to one of them, Friend, I do you no injury. Did you not agree with me for a denarius?
Amma mai gonar ya amsa wa daya daga cikin su, ya ce, 'Aboki na, ban yi maku laifi ba. Ai mun shirya zan biya ku yadda ake biya a yini, ko ba haka ba?
14 Take what is yours, and depart. It is my will to give to this last as much as to you.
Ku karbi abin da ke na ku, ku tafi. Ganin dama ta ne, in ba wadannan da suka zo a karshe daidai da ku.
15 And may not I do what I will with my own? Is your eye evil, because I am good?
Ashe, ba daidai bane a gare ni, in yi abin da na ga dama da mallaka ta? Ko kishi ne kuke yi saboda kirki na?'
16 Thus the last shall be first, and first last; for there are many called, but few chosen.
Haka yake, na karshe za su zama na farko, na farko kuma su zama na karshe.'' [An kira dayawa, amma kadan ne zababbu].
17 When Jesus was on the road to Jerusalem, he took the twelve aside, and said to them,
Da Yesu zai tafi Urushalima, ya dauki sha-biyun nan a gefe, yayin da suke tafiya, sai ya ce masu,
18 We are now going to Jerusalem, where the Son of Man shall be delivered to the chief priests and the scribes, who will condemn him to die,
“Ku duba fa, zamu tafi Urushalima, kuma za a bada Dan Mutum ga manyan firistoci da marubuta. Za su kuma yanke masa hukuncin kisa,
19 and deliver him to the Gentiles to be mocked, and scourged, and crucified; but the third day he will rise again.
za su kuma bada shi ga al'ummai don suyi masa ba'a, su bulale shi, su kuma gicciye shi. Amma a rana ta uku, za a tada shi.''
20 Then the mother of Zebedee's sons came to him with her sons, and, prostrating herself, entreated he would grant the request she had to make.
Sai uwar 'ya'yan Zabadi ta zo wurin Yesu tare da 'ya'yanta. Ta rusuna a gabansa tana neman alfarma a wurinsa.
21 He said to her, What do you wish? She answered, That, in your Reign, one of these my two sons may sit at your right hand, the other at your left.
Yesu ya ce mata, Me kike so in yi maki?'' Sai ta ce masa, ''Ina so ka ba 'ya'yana izinin zama a mulkinka, daya a hannun damanka, daya kuma a hannun hagunka.
22 Jesus replying, said, You know not what you ask. Can you drink such a cup as I must drink? They said to him, We can.
Amma Yesu ya amsa, ya ce, ''Baku san abin da kuke roko ba. Ko zaku iya sha daga cikin kokon da zan sha bada dadewa ba?'' Sai suka ce masa, ''Zamu iya.''
23 He answered, You shall indeed drink such a cup. But to sit on my right hand, and at my left, I can not give, unless to those for whom it is prepared by my Father.
Sai ya ce masu, ''In dai kokon nan da zan sha ne, lallai zaku sha. Amma, zama a hannun dama na da kuma hannun hagu na, ba ni ne mai bayarwa ba, amma na wadanda Uba na ya shirya domin su ne.''
24 The then, hearing this, were full of indignation against the two brothers;
Sa'anda sauran almajirai goma suka ji haka, sun yi bacin rai da 'yan'uwan nan biyu.
25 but Jesus, calling them to him, said, You know that the Princes of the nations domineer over them, and the great exercise their authority upon them.
Amma Yesu ya kira su wurin sa, ya ce, ''Kuna sane da cewa, sarakunan al'ummai suna gwada masu mulki, manyan-gari kuma na nuna masu iko.
26 It must not be so amongst you: on the contrary, whosoever would become great amongst you, let him be your servant;
Ba zai kasance haka a tsakanin ku ba. A maimakon haka, duk wanda ke da marmari ya zama da girma a tsakanin ku, ya zama baran ku.
27 and whosoever would be chief amongst you, let him be your slave:
Wanda kuma ke da marmari ya zama na farko a cikin ku, ya zama baran ku.
28 even as the Son of Man came not to be served, but to serve, and to give his life a ransom for many.
Kamar dai yadda Dan mutum bai zo don a bauta masa ba, amma yayi bauta, ya kuma bada ransa fansa domin mutane dayawa.''
29 As they left Jericho, followed by a great multitude,
Da suka fita daga Yariko, babban taro suka bi shi.
30 two blind men, who sat by the way-side, hearing that Jesus passed by cried, saying, Master, Son of David, have pity on us.
Suka kuma ga makafi biyu zaune a bakin hanya. Da makafin suka ji cewa Yesu ne ke wucewa, sai suka tada murya suna cewa, ''Ya Ubangiji, Dan Dauda, kayi mana jinkai.''
31 The multitude charged them to be silent: but they cried the louder, saying, Master, Son of David, have pity on us.
Amma jama'ar suka tsauta masu, suka ce suyi shiru. Duk da haka, makafin suka kara tada murya fiye da na da, suka ce, ''Ya Ubangiji, Dan Dauda, kayi mana jinkai.''
32 Then Jesus stopping, called them, and said, What do you want me to do for you?
Sai Yesu ya tsaya cik, ya sa aka kira su, sai ya ce masu, ''Me kuke so in yi maku?''
33 They answered, Sir, to make us see.
Sai suka ce masa, Ya Ubangiji, muna so mu sami ganin gari.''
34 Jesus had compassion and touched their eyes. Immediately they received sight, and followed him.
Sai Yesu yayi juyayi a cikin sa, ya taba idanunsu. Nan da nan, suka sami ganin gari, suka kuma bi shi.