< Matthew 12 >
1 At that time, as Jesus was walking through the corn on Sabbath, his disciples being hungry, began to pluck the ears of corn, and to eat them.
A wannan lokaci, Yesu ya tafi a ranar Asabaci, ya bi cikin gonar hatsi. Almajiransa na jin yunwa, sai suka fara zagar hatsi suna ci.
2 The Pharisees observing this, said to him, Lo! your disciples are doing what is not lawful to do on the Sabbath.
Amma da Farisawa suka gan su, sai su ka ce wa Yesu. “Duba, almajiranka su na yin abin da doka ta haramta a ranar Asabaci.”
3 He answered, Have you not read what David did, and his attendants, when they were hungry;
Amma Yesu ya ce masu, “Baku karanta abin da Dauda ya yi ba, lokacin da ya ke jin yunwa, tare da mazan da ke tare da shi?
4 how he entered the tabernacle of God, and eat the loaves of the presence, which was not lawful for him, or his attendants, to eat but solely for the priests?
Yadda ya shiga gidan Allah, ya ci gurasar alfarwa da doka ta hana shi ko mazan da ke tare da shi su ci, sai dai Firistoci ne kawai doka ta basu damar ci?
5 Or have you not learnt from the law, that the priests in the temple violate the rest to be observed on Sabbaths, and are blameless?
Sa'annan ba ku karanta cikin shari'a cewa, a ranar Asabaci, Firistoci da ke cikin haikali na sabawa ranar Asabaci, amma kamar ba su yi laifi ba?
6 Now I affirm, that something greater than the temple is here.
Amma ina tabbatar maku da cewa, wani wanda ya fi haikali girma yana nan.
7 But had you know what this means, "I desire humanity and not sacrifice," you would not have condemned the guiltless;
In da kun san ma'anar wannan 'Na fi son jinkai fiye da hadaya,' da baku shari'anta wa marar laifi ba.
8 for the Son of Man is master of the Sabbath.
Gama Dan mutum shine Ubangijin Asabaci.”
9 Leaving that place, he went into their synagogue,
Sa'annan Yesu ya bar wannan wuri, ya shiga majami'ar su.
10 and found a man there whose hand was blasted. They asked Jesus, with a design to accuse him, Is it lawful to heal on the Sabbath?
Sai ga wani mutum wanda hannun sa ya shanye, sai Farisawa suka tambayi Yesu, cewa, “Doka ta halarta a yi warkarwa a ranar Asabaci?” Domin su zarge shi a kan zunubi.
11 He answered, What man is there amongst you, who having one sheep, if it fall into a pit on the Sabbath, will not lay hold on it, and lift it out?
Yesu ya ce masu, “Wanene a cikin ku, wanda idan ya na da tunkiya guda, sa'annan tunkiyar nan ta fada a rami mai zurfi a ranar Asabaci ba zai kamo ta ya fitar da ita ba?
12 And does not a mean greatly excel a sheep? It is lawful, therefore, to do good on the Sabbath.
Yaya za a kwatanta darajar mutum da tunkiya! Saboda haka ya halarta a yi alheri ranar Asabaci.”
13 Then he said to the man, Stretch out your hand. And as he stretched it out, it became sound like the other.
Sai Yesu ya ce wa mutumin nan “Mika hannun ka.” Ya mike hannunsa, sai hannun nan ya dawo lafiyaye kamar dayan hannunsa.
14 But the Pharisees went out, and concerted against Jesus to destroy him.
Amma Farisawa su ka fita waje su ka fara mugun shiri domin sa. Su na neman hanyar da za su kashe shi.
15 Jesus knowing this, departed; and being followed by a vast multitude, healed all their sick,
Da Yesu ya fahimci wannan, sai ya janye kan sa daga nan. Mutane da dama su ka bi shi, ya warkar da su duka.
16 enjoining them not to make him known.
Ya dokace su da kada su bayyana shi ga kowa,
17 Thus the word of the Prophet Isaiah was verified,
domin ya zama gaskiyar abin da aka fada ta wurin annabi Ishaya, cewa,
18 "Behold my servant whom I have chosen, my beloved in whom my soul delights; I will cause my Spirit to abide upon him, and he shall give laws to the nations;
“Dubi, bawa na zababbe; kaunatacce na, wanda ya ke faranta mani raina sosai. Zan sa Ruhu na bisan sa, za ya furta hukunci zuwa al'ummai.
19 he will not contend, nor clamor, nor cause his voice to be heard in the streets.
Ba za ya yi jayayya ko tada murya ba, babu wanda za ya ji muryar sa a karabku.
20 A bruised reed he will not break; and a dimly burning taper he will not quench, till he render his laws victorious.
Ba zai karya kara da ya tankwashe ba; ba zai kashe fitilar da ta kusa mutuwa ba; sai ya kawo hukunci ga nasara.
21 Nations also shall trust in his name."
Sa'annan al'ummai za su dogara a ga sunansa.
22 Then was brought to him a demoniac, dumb, and blind, and he cured him, so that he both spoke and saw.
Sa'annan wani mutum, makaho ne, kurma kuma, aljannu kuma na cikinsa, an kawo shi wurin Yesu. Ya warkar da shi, ya sami ganin gari ya kuma yi magana.
23 And all the people said with amazement, Is this the son of David?
Jama'a su ka yi mamaki kwarai, su na cewa, “Ko wannan ne Dan Dawuda?”
24 But the Pharisees hearing them, said, This man expels demons only by Beelzebub, prince of the demons.
Amma da Farisawa su ka ji wannan al'ajibi, sai su ka ce, “Mutumin nan yana fitar da aljannu ta wurin Bahalzabuba sarkin aljannu ne.”
25 But Jesus, knowing their surmises, said to them, By intestine dissensions any kingdom may be desolated; and no city or family, where such dissensions are, can subsist.
Amma Yesu ya san tunanin su, sai ya ce. “Duk mulkin da ya rabu gaba da kan sa, ba zaya tsaya ba, duk wani birni da ya rabu ba zai tsaya ba, ko gida da ya tsage, za ya rushe.
26 Now if Satan expel Satan, his kingdom is torn by intestine dissensions; how can it then subsist?
Idan Shaidan ya fitar da Shaidan, ya rabu gaba da kansa. Yaya mulkin sa za ya tsaya?
27 Besides, if I expel demons by Beelzebub, by whom do your sons expel them? Wherefore they shall be your judges.
Idan Ina fitar da aljannu da ikon Ba'alzabuba, ta wurin wa masu bin ku su ke fitar da su? Saboda haka, su za su shari'anta ku.
28 But if I expel demons by the Spirit of God, the Reign of God has overtaken you.
Amma idan ina fitar da aljannu da Ruhun Allah ne, hakika mulkin Allah ya zo gare ku.
29 For how can one enter the strong one's house, and plunder his goods, unless he first overpower the strong one? Then indeed he may plunder his house.
Kuma ta yaya mutum za ya shiga gidan mai karfi ya kwashe masa kaya ba tare da ya fara daure shi ba? Sa'annan ne za ya iya satar masa kaya daga gidansa.
30 He who is not for me, is against me; and he who gathers not with me, scatters.
Wanda baya tare da ni yana gaba da ni ke nan, wanda kuma baya tarawa tare da ni, yana watsarwa ne.
31 Wherefore I say to you, though every other sin and detraction in men is pardonable, their detraction from the Spirit is unpardonable:
Saboda haka ina ce maku, kowanne zunubi da sabo, za a gafarta wa mutum, amma sabon Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta shi ba.
32 for whosoever shall inveigh against the Son of Man may obtain pardon; but whosoever shall speak against the Holy Spirit, shall never be pardoned, either in the present state or the future. (aiōn )
Duk wanda yayi batanci ga Dan Mutum, za a gafarta masa. Amma duk wanda yayi batanci game da Ruhu Mai Tsarki ba za a gafarta masa ba, a nan duniya da har abada. (aiōn )
33 Either call the tree good, and its fruit good; or call the tree bad, and its fruit bad: for we distinguish the tree by its fruit.
Ko dai a mai da itace mai kyau 'ya'yansa kuma su yi kyau, ko a mai da itace marar kyau 'ya'yansa kuma marasa kyau, gama ana sanin itace ta wurin 'ya'yansa.
34 Offspring of vipers! how can you that are evil speak good things, since it is out of the fullness of the heart that the mouth speaks.
Ku 'ya'yan macizai, tun da ku miyagu ne, yaya za ku iya fadin abubuwa nagari? Gama daga cikar zuciya baki ke magana.
35 The good man, out of his good treasure, produces good things; the bad man, out of his bad treasure, produces bad things.
Mutumin kirki daga ajiyar zuciyarsa ya kan fitar da abubuwa masu kyau, mugun mutum kuma daga mummunar ajiyar zuciyarsa ya kan fitar da abubuwan mugunta.
36 Be assured, however, that of every pernicious word which men shall utter, they shall give an account on the day of judgment.
Sa'annan ina ce maku a ranar shari'a, mutane za su bada lissafin abubuwan banza da su ka fadi.
37 For by your words you shall be acquitted, and by your words you shall be condemned.
Gama ta wurin maganganun ku, za a 'yantar da ku, ta wurin maganganun ku kuma za a kashe ku.”
38 Then some of the Scribes and Pharisees interposed, saying, Rabbi, we desire to see a sign for you.
Sa'annan wadansu Malaman Attaura, da Farisawa suka amsa suka ce wa Yesu, “Mallam, muna so mu ga wata alama daga gare ka.”
39 He answering, said to them, An evil and adulterous race demands a sign; but no sign shall be given it, but the sign of the Prophet Jonah.
Amma Yesu ya amsa ya ce masu, “Mugun zamani da mazinaciyar tsara, su na bukutar alama. Amma babu alamar da za a ba su, sai dai alamar annabi Yunusa.
40 For as Jonah was three days and three nights in the stomach of the great fish, the Son of Man will be three days and three nights in the bosom of the earth.
Gama yadda Yunusa ya yi kwana uku da dare uku a cikin babban kifi, haka ma Dan Mutum zaya yi kwana uku da dare uku a cikin zuciyar kasa.
41 The Ninevites will stand up in the judgment against this race, and cause it to be condemned, because they reformed when they were warned by Jonah; and behold here something greater than Jonah.
Mutanen Nineba za su tsaya a ranar shari'a da wannan zamani sannan su kashe su. Domin sun tuba da suka ji wa'azin Yunusa, amma duba wanda ya fi Yunusa yana nan.
42 The Queen of the South country will arise in the judgment against this race, and cause it to be condemned; because she came from the extremities of the earth to hear the wise discourses of Solomon; and behold here something greater than Solomon.
Sarauniyar Kudu za ta tashi da mutanen wannan zamani ta kuma kashe su. Ta zo daga karshen duniya domin ta ji hikimar Sulaimanu, kuma duba, wanda ya fi Sulaimanu yana nan.
43 An unclean spirit, when he is gone out of a man, wanders over the parched deserts in search of a resting-place. And not finding any,
Idan kazamin ruhu ya rabu da mutum, ya kan wuce ya nemi wuraren da ruwa yake domin ya huta, amma bai samu ba.
44 he says, I will return to my house whence I came; and being come, he finds it empty, swept, and garnished.
Sai ya ce, 'zan koma gidana inda na fito'. Bayan ya dawo, sai ya tarar da gidan nan an share shi ya zama da tsabta.
45 Then he goes, and brings with him seven other spirits more wicked than himself; and having entered, they dwell there; and the last state of that man is worse than the first: thus will it fare with this evil race.
Sai ya koma ya kawo wadansu ruhohi guda bakwai, wadanda su ka fi shi mugunta, sa'annan dukan su su zo su zauna a nan. Sa'annan yanayin mutumin nan na karshe ya fi na farko muni. Haka zaya kasance ga wannan mugun zamani.
46 While he discoursed to the people, his mother and brothers were without, desiring to speak with him.
Sa'adda Yesu ya ke yi wa Jama'a jawabi, sai mahaifiyarsa da 'yan'uwansa su ka zo su ka tsaya a waje, suna neman su yi magana da shi.
47 And one said to him, Your mother and your brothers are without, desiring to speak with you.
Sai wani ya ce masa, “Duba, mahaifiyarka da 'yan'uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai”.
48 He answering, said to him that told him, Who is my mother? and who are my brothers?
Amma Yesu ya amsa ya ce wa shi wanda ya gaya masa, “Wacece mahaifiyata? Kuma su wanene 'yan'uwana?”
49 The stretching out his hand toward his disciples, he said, Behold my mother and my brothers.
Sai ya mika hannu ya nuna almajiransa ya ce, “Duba, ga mahaifiyata da 'yan'uwana!
50 For whosoever does the will of my Father who is in heaven, is my brother, and sister, and mother.
Gama duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda ya ke cikin sama, shine dan'uwana, da 'yar'uwata da mahaifiyata.”