< Mark 1 >
1 The beginning of the gospel of Jesus Christ, Son of God.
Wannan itace farkon bisharar Yesu Almasihu, Dan Allah.
2 As it is written in Isaiah the Prophet, "Behold, I send my messenger before thee, who shall prepare thy way:"
kamar yadda aka rubuta cikin littafin annabi Ishaya. Duba, ina aika manzona, a gabanka, wanda zai shirya maka hanya.
3 "The voice of one proclaiming in the wilderness, Prepare a way for the Lord, make for him a straight passage:"
Akwai murya mai kira a jeji, tana cewa ka shirya hanyar Ubangiji. ka daidaita ta.
4 thus came John immersing in the wilderness, and publishing the immersion of reformation for the remission of sins.
Yahaya ya zo, yana baptisma acikin jeji yana wa'azin tuba, domin gafarar zunubai.
5 And all the country of Judea, and the inhabitants of Jerusalem, resorted to him, and were immersed by him in the river Jordan, confessing their sins.
Dukan kasar Yahudiya da mutanen Urshalima suka zo wurin sa, a ka kuma yi masu baptisma a kogin urdun. suna furta zunubansu.
6 Now John's clothing was of camel's hair, tied around his waist with a leather girdle: and he lived upon locusts and wild honey.
Yahaya yana saye da tufa ta gashin rakumi, yana kuma da damara ta fata a kugunsa, abincinsa fara ce da zuma.
7 And he proclaimed, saying, One mightier than I comes after me, whose shoe-latchet I am unworthy to stoop down and untie.
Yana wa'azi, ya ce “akwai mai zuwa a bayana wanda ya ke da iko fiye da ni. wanda ko maballin takalminsa ban isa in kwance ba.
8 I, indeed, have immersed you in water; but he will immerse you in the Holy Spirit.
Ni ina yi maku baptisma da ruwa, amma mai zuwa a bayana zai yi maku baptisma da Ruhu Mai Tsarki''.
9 At that time Jesus came from Nazareth of Galilee to the Jordan, and was immersed by John.
Sai ya kasance a kwanakin nan Yesu ya zo daga Nazarat ta Galili, sai Yahaya ya yi masa baptisma a kogin urdun.
10 As soon as he arose out of the water, he saw the sky part asunder, and the Spirit descend upon him like a dove.
Sa'adda Yesu ya fito daga ruwan, sai sama ta bude, sai Ruhu ya sauko a bisansa da kamanin kurciya.
11 And a voice from heaven, which said, Thou art my Son, the beloved, in whom I delight.
Sai wata murya ta zo daga sama, tana cewa, “Kai kaunataccen Dana ne. zuciyata ta na murna da kai kwarai''.
12 Immediately after this, the spirit conveyed him into the wilderness;
Sai Ruhu ya iza shi zuwa jeji.
13 and he continued in the wilderness forty days tempted by Satan; and was among the wild beasts; and the heavenly messengers ministered to him.
Yana a jeji kwana arba'in, Shaidan yana jarabtar sa. Yana cikin jeji da dabobi, sai malaiku su ka yi masa hidima.
14 But after John's imprisonment, Jesus went to Galilee, proclaiming the good tidings of the Reign of God.
Bayan da aka kama Yahaya, Yesu ya shiga kasar Galili yana wa'azin bisharar Allah.
15 The time, he said, is accomplished, the Reign of God approaches; reform, and believe the good tidings.
Yana cewa, “Lokaci ya yi, gama mulkin Allah ya kusato. Ku tuba ku bada gaskiya ga bishara”.
16 Then walking by the sea of Galilee, he saw Simon, and Andrew, Simon's brother, casting a drag net into the sea, for they were fishers.
Sa'adda ya ke wucewa a gefen takun Galili, sai ya ga Saminu da Andarawus, dan'uwansa suna jefa taru a teku, domin su masunta ne.
17 Jesus said to them, Come with me, and I will cause you to be fishers of men.
Yesu ya ce masu ku zo, ku biyo ni, ni kuwa sai in maisheku masuntan mutane”.
18 Immediately they left their nets, and followed him.
Nan da nan suka bar tarun su, suka bi shi.
19 Passing on a little, and seeing James, son of Zebedee, with John his brother, who were mending their nets in a bark,
Sa'adda Yesu ya yi tafiya kadan, sai ya ga Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan'uwansa; suna gyaran tarunsu a jirgin ruwa.
20 he immediately called them; and leaving their father Zebedee in the bark with the hired servants, they accompanied him.
Sai ya kira su, su kuwa suka bar mahaifinsu Zabadi a jirgin ruwan da ma'aikatansu, sai su ka bi shi.
21 And they went to Capernaum; and on the Sabbath he repaired directly to the synagogue, and instructed the people,
Da su ka shigo cikin kafanahum, a ranar asabar, Yesu ya shiga majami'a ya koya masu.
22 who were filled with admiration at his manner of teaching; for he taught as one having authority, and not as the scribes.
Su ka yi mamakin koyarwarsa, domin ya na koya masu da iko ba kamar marubuta ba.
23 Now there was in their synagogue a man possessed with an unclean spirit, who cried out,
A nan cikin majami'a akwai wani mutum mai kazamin ruhu, sai ya yi ihu da karfi.
24 Ah! Jesus of Nazareth, what hast thou to do with us? Art thou come to destroy us? I know who thou art, the Holy One of God.
Yana cewa Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo ne domin ka halakar da mu? Na san wanene kai. Kai ne Mai Tsarki na Allah”.
25 Jesus rebuking him, said, Be silent, and come out of him.
Sai Yesu ya tsauta wa kazamin ruhun ya ce, “Ka yi shiru ka fita daga cikinsa”.
26 Then the unclean spirit threw him into convulsions; and, raising loud cried, came out of him:
Bayan da kazamin ruhun ya buga shi kasa, sai kazamin ruhun ya yi ihu sa'annan ya fita daga jikinsa.
27 at which they were all so amazed, that they asked one another, What does this mean? For he commands with authority even the unclean spirits, and they obey him.
Sai dukan mutanen su ka yi mamaki kwarai, suna tambayar junansu menene wannan? wace sabuwar koyarwa ce da iko haka? har yana umartar kazaman ruhohi suna kuwa yi masa biyayya!”
28 And thenceforth his fame spread through all the region of Galilee.
Nan da nan labarinsa ya bazu ko'ina a dukkan kewayen kasar Galili.
29 As soon as they were come out of the synagogue, they went with James and John into the house of Simon and Andrew,
Bayan da suka bar majami'a, sai su ka shiga gidan Saminu da Andarawus, suna kuma tare da Yakubu da Yahaya.
30 where Simon's wife's mother lay sick of a fever, of which they immediately acquainted Jesus.
Surikar Saminu tana kwance ba lafiya tana fama da zazzabi. Sai suka gaya wa Yesu game da ita.
31 And he came, and taking her by the hand, raised her; instantly the fever left her, and she entertained them.
Sai ya zo, ya kama hannunta, ya daga ta, sai zazzabin ya sake ta, ta fara yi masu hidima.
32 In the evening, after sunset, they brought to him all the sick, and the demoniacs;
Da yamman nan, bayan da rana ta fadi, sai su ka kawo masa dukan marasa lafiya da masu fama da aljanu.
33 the whole city being assembled at the door.
Dukan mutanen garin su ka taru a bakin kofa.
34 And he healed many persons affected with various diseases, and expelled many demons, whom he permitted not to speak, because they knew him.
ya warkar da masu ciwo da yawa da masu chututtuka iri-iri, ya kuma fitar da bakaken aljanu, amma bai yarda aljanun su yi magana ba domin sun san shi.
35 On the morrow, having risen before dawn, he went out, and retired to a solitary place, and prayed there.
Ya tashi da sassafe, tun da sauran dare, ya tafi wurin da ba kowa, a can ya yi add'ua.
36 And Simon and his company went in quest of him,
Saminu da wandanda suke tare da shi suka neme shi.
37 and having found him, said to him, Every person seeks you.
Suka sa me shi, sai su ka ce masa, “kowa yana nemanka”.
38 Jesus said, Let us go to the neighboring boroughs, to make proclamation there also: for I came out with this design.
Ya ce, bari mu tafi wani wuri, zuwa wadansu garuruwan da ke kewaye, Saboda in yi wa'azi a can kuma. Wannan shi yasa na zo nan''.
39 Accordingly he proclaimed in their synagogues throughout all Galilee, and expelled demons.
Ya tafi dukan kasar Galili, yana wa'azi a majimi'un su yana kuma fitar da aljanu.
40 And a leper came to him, and on his knees entreated him, saying, If you will, you can cleanse me.
Wani kuturu ya zo wurinsa. Yana rokonsa, ya durkusa. Ya ce masa, “in ka yarda kana iya warkar da ni.
41 Jesus had compassion, and stretching out his hand and touching him, said, I will, be you clean.
Sai ya yi juyayi, Yesu ya mi ka hannun sa ya ta ba shi ya na ce masa “Na yarda. Ka sarkaka”.
42 This he had no sooner uttered, than the leprosy departed from the man, and he was cleansed.
Nan da nan kuturtar ta barshi, ya kuma sa mu tsarkakewa.
43 Then Jesus strictly charging him, and dismissing him,
Yesu ya yi masa gargadi sosai, ya salame shi.
44 said, See you tell nothing of this to any man; but go, show yourself to the priest; and offer for your cleansing the things prescribed by Moses, that it may be notified to the people.
Ya ce masa “ka tabbata fa kada ka gayawa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, sai ka je ka yi hadaya domin tsarkakewa kamar yadda Musa ya umurta, domin shaida.
45 But the man, as soon as he was gone, began to blaze this story, talking openly everywhere, insomuch that Jesus could no longer publicly appear in the city; but remained without in solitary places, whither the people resorted to him from all parts.
Amma da ya fita sai ya fara gaya wa kowa, ya baza maganar a ko'ina, har Yesu bai iya tafiya a sake a garin ba. Ya tafi ya tsaya a wuraren da ba kowa, mutane kuwa su ka zo wurinsa daga ko'ina.