< Luke 8 >

1 Afterward he traveled through cities and villages, proclaiming the joyful tidings of the Reign of God, being attended by the twelve,
Bayan haka, Yesu da almajiransa goma sha biyu, su ka zagaya cikin birane da kauyuka dabam dabam, suna wa'azi da shelar labari mai dadi game da mulkin Allah,
2 and by certain women, who had been delivered from evil spirits and distempers; Mary, called Magdalene, out of whom went seven demons;
mata da yawa wadanda Yesu ya warkar daga aljanu da cututtuka iri iri suna tafiya tare da su. A cikinsu akwai Maryamu wadda a ke ce da ita Magadaliya, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta,
3 Joanna, wife of Chuza, Herod's steward; Susanna, and several others, who assisted him with their property.
da Yuwana matar Kuza wakilin Hirudus, da Suzanatu da kuma wasu mata da yawa. Daga abin hannunsu suka tanada masu.
4 Now, when a great multitude was assembled, and the people were flocking to him, out of the cities, he spoke by a parable.
Wata rana aka tara taron mutane da yawa, saboda mutane su na zuwa daga birane da yawa domin su ga Yesu. Ya yi magana dasu cikin misali.
5 The sower went out to sow his grain: and in sowing, part fell by the way-side, and was crushed under foot, or picked up by the birds;
“Wani mai shuka ya tafi domin ya shuka iri. Sa'adda ya ke yafa iri, wadansu iri suka fada a kan hanya. Sai mutane suka tattake su, tsuntsaye kuma suka tsince wadansu suka cinye.
6 part fell upon a rock, and when it was sprung up, withered away for want to moisture;
Wadansu kuma suka fada a kan duwatsu inda babu kasa da yawa. Da suka tsaro suka fara girma, sai nan da nan suka bushe saboda babu laima a wurin.
7 part of it also fell among thorns, and the thorns grew up and choked it;
Wadansu irin kuma suka fada inda yake da kayayuwa. Tsiretsiren kayayuwan suka fito tare da irin da aka shuka, suka shake su yadda basu iya yin girma ba.
8 and part fell into good soil, and sprung up, and yielded increase, a hundred fold. Having said this, he cried, Whosoever has ears to hear, let him hear.
Amma wadansu irin suka fada a kan kasa mai kyau, suka yi girma sosai suka ba da anfani da yawa, har rubi dari.” Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi kira gare su, “Duk mai kunnen ji, bari ya ji.”
9 And his disciples asked him, saying, What does this parable mean?
Sai almajiran Yesu suka tambaye shi ya gaya ma su ma'anar labarin.
10 He answered, It is your privilege to know the secrets of the Reign of God, which, to others, are couched in parables; that, though they look, they may not perceive; that though they hear, they may not understand.
ya ce da su, “Ku aka ba dama ku gane boyayyun abubuwa, na mulkin Allah. Amma ga sauran mutane ina yi masu magana cikin misalai, 'Domin ko da sun gani ba za su gane ba, kuma ko da sun ji ba za su fahimta ba.”
11 Now, this is the meaning of the parable. The seed is the word of God.
To ga ma'anar misalin. Irin shi ne maganar Allah.
12 By the wayside are meant those hearers out of whose hearts the devil coming, takes away the word, these they should believe, and be saved.
Irin da ya fada a kan hanya sune mutanen da suka ji maganar Allah amma daga baya sai shedan ya zo ya dauke maganar daga cikin hankulansu, domin kada su bada gaskiya su tsira.
13 By the rock are meant those, who, when they hear, receive the word with joy; yet not having it rooted in them, are but temporary believers; for in the time of trial they fall off.
Sa'annan, wadanda suka fada kan duwatsu sune mutanen da, da zarar sun ji maganar, sukan karbe ta da murna, amma ba su da sauyu; su kan bada gaskiya na dan lokaci kadan kawai, da zaran gwaji ya same su sai su ridda.
14 By the ground incumbered with thorns, are meant those hearers who are entangled in the business, and pursuits, and pleasures of life; which stifle the word, so that it brings no fruit to maturity.
Irin da suka fada cikin kayayuwa, sune mutanen da suka ji maganar, amma da suka ci gaba da rayuwa, sai suka bari matsalolin rayuwa kamar dukiya da jin dadin rayuwa suka fi karfinsu, sai ya zama ba su iya bada 'ya'yan da suka yi girma ba.
15 But by the good soil are meant those, who, having heard the word, retain it in a good and honest heart, and persevere in bringing forth fruit.
Amma irin da suka fada a kan kasa mai kyau, wadannan sune mutanen da suka ji maganar, suka karbe ta da gaskiya da zuciya daya, sun rike ta kam-kam, suna jimrewa wurin ba da 'ya'ya.
16 A lamp is never lighted to be covered with a vessel, or put under a bed; but to be set on a stand, that they who enter may see the light.
Ba mai kunna fitila, ya rufe ta da kasko, ko su sa ta a karkashin gado. Amma sai a sa ta a wurin zaman ta domin duk wanda ya shigo ya iya ganin hasken ta.
17 For there is no secret which shall not be discovered; nor anything concealed which shall not be known, and become public.
Babu abin da yake a boye wanda ba za a tone shi ba, ko wani asiri da ba za ya fito fili a san shi ba.
18 Take heard, therefore, how you hear; for to him who has, more shall be given; but from him who has not, shall be taken even that which he seems to have.
Ku yi hankali da yadda kuke ji, domin duk mai abu, shi za a kara wa, kuma duk mara abu, dan kadan da yake tunani yana da shi ma, za a dauke.”
19 Then his mother and brothers came to speak with him; but could not get near him for the crowd.
Sai mahafiyar Yesu da 'yan'uwansa, su ka zo wurinsa, amma ba su iya zuwa ko kusa da shi ba saboda taron jama'a.
20 And it was told him by some persons, Your mother and your brothers are without, desiring to see you.
Sai wani ya gaya masa, “Ga mahaifiyarka da 'yan'uwanka, su na tsayuwa a waje, su na son ganin ka.”
21 But he, answering, said to them, My mother and my brothers are those who hear the word of God, and obey.
Amma Yesu ya amsa ya ce ma su, “Mahaifiyata da 'yan'uwana sune wadanda suke jin maganar Allah, suke yin biyayya da ita.”
22 One day, Jesus having gone into a bark with his disciples, said to them, Let us cross the lake. Accordingly they set sail.
Wata rana kuma Yesu ya shiga cikin jirgin ruwa, shi da almajiransa. Ya ce masu, “Ina so mu je dayan ketaren tafkin.” Sai su ka fara tafiya domin su ketare tafkin.
23 But while they sailed, he fell asleep; and there blew such a storm upon the lake, as filled the bark with water, and endangered lives.
Amma sa'adda su ke tafiya sai Yesu ya yi barci, sai wata iska mai karfi ta taso cikin tafkin, nan da nan sai jirgin ya fara cika da ruwa, kuma su na cikin hatsari.
24 And they came to him, and awakened him, saying, Master, Master, we perish! Then he arose and rebuked the wind, and the raging of the water: and they ceased, and there was a calm.
Sai almajiran Yesu su ka zo su ka tashe shi daga barci. Suka ce da shi, “Ya Shugaba! Ya Shugaba! Za mu mutu!” Sai ya tashi ya umarci iskar, sai iskar mai hauka da tumbatsar ruwan sun tsaya tsit.
25 And Jesus said to them, Where is your faith? But they said one to another, with fear and admiration, Who is this that commands even the winds and the water, and they obey him?
Daga nan sai ya ce da su, “Ina bangaskiyar ku?” Almajiran suka tsorata suka yi mamakin abin da ya faru nan take. Suka ce wa junansu, “Wanene wannan wanda har zai ba iska da ruwa umarni kuma su yi masa biyayya?”
26 And they arrived at the country of the Gadarenes, which is opposite to Galilee.
Suka zo yankin Garasinawa, wanda ke kusa da Gallili.
27 Being come ashore, a man of the city met him, who had been long possessed by demons; and who wore no clothes, and had no habitation but the sepulchers.
Sa'adda Yesu ya sauka kasa, sai wani mutum daga wannan yankin ya tarbe shi. Wannan mutum kuwa yana da aljanu. Mutumin ya dade ba ya sa tufafi, kuma ba ya zama a gida. Maimakon haka, sai a cikin kabarbura ya ke zama.
28 When he saw Jesus, he roared out, and threw himself at his feet, crying, What have you to do with me, Jesus, Son of the Most High God? I beseech you, do not torment me.
Sa'adda ya ga Yesu, mutumin ya yi ihu da karfi, ya rusuna a gabansa da babban murya ya ce, “Me zan yi da kai, Yesu, Dan Allah Madaukaki? Ina rokonka, kada ka ba ni azaba!”
29 (For he had ordered the unclean spirit to come out of the man; for it had frequently seized him, so that when he was chained and fettered, he broke his bonds, and was driven by the fiend into the desert.)
Domin Yesu ya umarci aljanun su fita daga cikinsa, domin sau da dama aljanun sukan kama shi. Ko an daure mutumin da sarkoki an kuma tsare shi, yakan tsuttsunke su, kazaman ruhohin sukan kora shi cikin jeji.
30 Then Jesus asked him, saying, What is your names?" He answered, Legion; because many demons had entered into him.
Sa'annan Yesu ya tambaye shi, “Yaya sunanka?” Sai ya ba da amsa, “Suna na dubbai.” Ya ce haka ne domin aljanu da yawa sun shiga wannan mutum.
31 And they entreated him, that he would not command them to go into the deep; (Abyssos g12)
Aljanun suka yi ta rokon Yesu kada ya ummarce su su shiga cikin rami mai zurfi. (Abyssos g12)
32 but, as there was a numerous herd of swine feeding on the mountain, that he would permit them to enter into the swine. And he permitted them.
Akwai babban garken aladu su na kiwo a kan tsauni kusa da wurin. Aljanun suka roki Yesu da ya barsu su shiga cikin aladun, shi kuwa ya yarda masu.
33 Then the demons having quitted the man, entered into the swine; and the herd rushed down a precipice into the lake, and were drowned.
Aljanun suka bar mutumin suka shiga cikin aladun, sai garken aladun suka gangara kwari suka fada cikin tafkin, suka nutse.
34 The herdsmen, seeing this, fled, and spread the news through the city and villages.
Lokacin da mutanen da su ke kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka gudu! Suka ba da rahoton abin da ya faru ga mutanen cikin gari da na wannan kewayen.
35 And the inhabitants flocked out to see what had happened. Being come to Jesus, and finding the man of whom the demons were dispossessed, sitting at the feet of Jesus, clothed, and in his right mind, they were afraid.
Don haka, mutanen da suka ji haka suka tafi domin su ga abin da ya faru, suka zo wurin da Yesu yake, suka ga mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa. Suka ga ya na sanye da tufafi, kuma ya na cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 But having been informed by the spectators, in what manner the demoniac delivered,
Mutanen da suka ga abin da ya faru, suka gaya wa wadansu yadda aka warkar da mutumin da aljanu suke iko da shi.
37 all the people of the country of the Gadarenes, entreated him to leave them; for they were struck with terror. Accordingly, he re-entered the bark, and returned.
Sai dukan mutane wadanda suke cikin yankin Garasinawa da wadanda suke kewaye, suka roki Yesu da ya fita daga cikin yankin kasarsu domin sun ji tsoro kwarai da gaske. Daga nan Yesu da almajiransa suka shiga cikin jirgin ruwa suka koma.
38 Now, the man out of whom the demons were gone, entreated his permission to attend him. But Jesus dismissed him, saying,
Mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa, ya roki Yesu cewa, “Ka barni in tafi tare da kai!” Amma Yesu ya sallame shi cewa,
39 Return home, and relate what great things God has done for you. Then he departed, and published through all the city, what great things Jesus had done for him.
“Ka koma gida ka gaya wa mutanen ka abubuwa masu girma wadanda Allah ya yi maka.” Daga nan sai mutumin ya tafi yana ta gayawa dukan mutanen birnin game da abubuwan da Yesu ya yi masa.
40 Jesus, at his return, was welcomed by the crowd, who were all waiting for him.
Sa'adda Yesu ya dawo, mutanen suka marabce shi, gama, dukansu suna jiransa.
41 Meantime, a man named Jairus, came, a ruler of the synagogue, who, throwing himself at the feet of Jesus, besought him to come into his house;
Sai ga wani mutum mai suna Yayirus, daya daga cikin shugabannin majami'a, ya zo kusa da Yesu ya rusuna da kansa a kasa. Ya roke shi domin ya zo gidansa,
42 for he had an only daughter, about twelve years old, who was dying. As Jesus went along, the people crowded him;
saboda diyarsa mai kimanin shekara goma sha biyu ta na bakin mutuwa, kuma ita kadai ce diya a gare shi. Amma sa'adda yake tafiya, taron mutane da yawa suna matsa shi.
43 and a woman, who had been twelve years afflicted with an issue of blood, and had consumed all her living upon physicians, none of whom could cure her,
Akwai wata mace a nan wadda take zubar jini har shekara goma sha biyu. Ta kashe kudinta duka a wurin likitoci, domin su warkar da ita amma ba wanda ya iya warkar da ita.
44 coming behind, touched the tuft of his mantle; upon which her issue was stopped.
Sai ta biyo ta bayan Yesu ta taba habar rigarsa. Nan take sai zubar jinin ya tsaya.
45 Then Jesus said, Who touched me? When every body denied it, Peter, and those with him, answered, Master, the multitude throng and press you, and do you say, Who touched me?
Yesu ya ce, “Wanene ya taba ni?” Wadanda suke kewaye da shi, kowa ya ce bai taba shi ba, Bitrus ya ce, “Shugaba, mutane da yawa suna ta taruwa kewaye da kai suna ta matsowa kusa da kai.”
46 Jesus replied, Some person has touched me; for I am sensible that my power was just now exerted.
Amma Yesu ya ce, “Na sani, wani ya taba ni, domin iko ya fita daga wurina.”
47 Then the woman perceiving that she was discovered, came trembling, and having thrown herself prostrate, declared to him, before all the people, why she had touched him, and how she had been immediately healed:
Sa'adda matar ta gane cewa ba za ta iya boyewa ba, sai ta zo wurinsa cikin tsoro. Ta durkusa a gaban Yesu, ta fada a gaban dukan jama'a dalilin da ya sa ta taba shi kuma nan da nan ta warke.
48 and he said to her, Daughter, take courage, your faith has cured you, go in peace.
Sai ya ce da ita, “Diya, bangaskiyarki ta warkar da ke. Tafi cikin salama.”
49 While he was yet speaking, one came from the house of the director of the synagogue, who said, your daughter is dead; trouble not the Teacher.
Yana cikin yin magana, wani daga cikin gidan shugaban majami'ar ya zo, ya ce, “Diyarka ta riga ta mutu, kada ka dami malam.”
50 Jesus, hearing this, said to Jairus, Fear not; only believe, and she shall be well.
Amma sa'adda Yesu ya ji haka, sai ya ce da shi, “Kada ka ji tsoro. Ka bada gaskiya za ta rayu.”
51 Being come to the house, he allowed no person to enter with him, except Peter, and John, and James, and the maid's father and mother.
Sa'adda ya zo gidan, bai bar kowa ya shiga gidan tare da shi ba sai Bitrus da Yahaya da Yakubu, da mahaifiyar yarinyar da babanta.
52 And all wept, and lamented her. But he said, Weep not; she is not dead, but asleep.
Dukan mutane a wurin, suna ta kuka da karfi saboda sun damu da yarinyar ta mutu. Amma Yesu ya ce da su, “Ku dena kuka! Ba mutuwa ta yi ba! Barci ta ke yi kawai!”
53 And they derided him, knowing that she was dead.
Mutanen suka yi ma sa dariyan reni, saboda sun sani yarinyar ta mutu.
54 But he, having made them all retire, took her by the hand, and called, saying, Maiden, arise.
Amma ya kama hannun ta yayi kira cewa, “Yarinya, na ce ki tashi!”
55 And her spirit returned, and she arose immediately, and he commanded to give her food.
Nan da nan ruhun ta ya dawo jikin ta sai ta tashi. Ya ce masu su ba ta wani abu ta ci.
56 And her parents were astonished, but he charged them not to mention to any person what had happened.
Iyayenta suka yi mamaki, amma Yesu ya ce da iyayen kada su gaya wa kowa abin da ya faru.

< Luke 8 >