< Luke 16 >

1 He said, likewise, to his disciples, A certain rich man had a steward, who was accused to him of wasting his estate.
Yesu ya kuma ce wa almajiransa, “Akwai wani mai arziki da yake da wakili, sai aka yi karan sa da cewa wannan wakili yana fallasar masa da dukiya.
2 Having, therefore, called him, he said, What is this that I hear of you? Render an account of your management, for you shall be steward no longer.
Sai mai arziki ya kira shi ya ce masa, 'Labarin me nake ji game da kai? Kawo lissafin wakilcin ka, don ba za ka sake zama wakili na ba.'
3 And the steward said within himself, What shall I do? My master takes from me the stewardship; I can not dig, and am ashamed to beg.
Sai wakilin ya ce a ransa, 'Kaka zan yi, da yake maigida na zai karbe wakilci daga hannuna? Gashi, ba ni da karfin noma ina kuwa jin kunya in yi roko.
4 I am resolved what to do, that when I am discarded, there may be some who will receive me into their houses.
Na san abin da zan yi domin idan an fitar da ni daga wakilcin, mutane su karbe ni a gidajensu.
5 Having, therefore, sent severally for all his master's debtors, he asked one, How much do you owe my master?
Sai wakilin ya kira kowanne daya da maigidansa ke bi bashi, yace wa na farkon, 'Nawa maigida na yake bin ka?'
6 He answered, A hundred baths of oil. Take back your bill, said the steward, sit down directly, and write fifty.
Ya ce, 'Garwan mai dari.' Sai ya ce masa, 'Ga takardarka, maza ka zauna, ka rubuta hamsin.'
7 Then he asked another, How much do you owe? He answered, A hundred homers of wheat. Take back your bill, said he, and write eighty.
Ya kuma ce wa wani, 'Nawa ake binka?' Ya ce, 'Buhu dari na alkama.' Ya ce masa, 'Ga tarkardarka, ka rubuta tamanin.'
8 The master commended the prudence of the unjust steward; for the children of this world are more prudent in conducting their affairs, than the children of light. (aiōn g165)
Sai maigida ya yaba wa wakilin nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama 'ya'yan zamanin nan a ma'ammalar su da mutanen zamaninsu sun fi 'ya'yan haske wayo. (aiōn g165)
9 Therefore, I say to you, with the deceitful riches procure to yourself friends, who, after your discharge, may receive you into the eternal mansion. (aiōnios g166)
Ina gaya maku ku yi abuta ta dukiya ta rashin gaskiya, saboda idan ya kare, su karbe ku a gidaje masu dauwama. (aiōnios g166)
10 Whoso is faithful in little is faithful also in much: and whoso is unjust in little, is unjust also in much.
Wanda yake da aminci a karamin abu, mai aminci ne a babban abu, wanda yake marar gaskiya a karamin abu, marar gaskiya ne a babban abu.
11 If, therefore, you have not been honest in the deceitful, who will intrust you with the true riches?
Idan fa ba ku yi aminci da dukiya mara adalci ba, wa zai amince maku da dukiya ta gaskiya?
12 And if you have been unfaithful managers for another, who will give you anything to manage for yourselves?
Idan kuma ba ku yi aminci da kudin wani ba, wa zai ba ku kudin da ke naku?
13 A servant can not serve two masters: for either he will hate one, and love the other; or, at least, will attend one, and neglect the other. You can not serve God and mammon.
Ba bawan da zai iya bauta wa iyayengiji biyu, ko dai ya ki daya, ya so daya ko kuwa ya amince wa dayan, ya raina dayan. Ba za ku iya bauta wa Allah ku kuma bauta wa dukiya ba.”
14 When the Pharisees, who loved money, heard all these things, they ridiculed him.
Da Farisawa da ke da kaunar kudi suka ji dukan wadannan abubuwa, suka yi masa ba'a.
15 But he said to them, As for you, you make yourselves pass upon men for righteous, but God knows your hearts; for that which is admired of men is abhorred of God.
Sai ya ce masu, “Ku ne masu baratar da kanku a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abin da mutane suke girmamawa kwarai abin kyama ne a gun Allah.
16 You had the law and the prophets till the coming of John, since whose time, the kingdom of God is announced, and every occupant enters it by force.
Attaura da litattafan annabawa suna nan har zuwan Yahaya. Tun daga lokacin nan ake yin bisharar mulkin Allah, kowa kuma yana kokarin kutsawa zuwa cikinta.
17 But sooner shall heaven and earth perish, than one tittle of the law shall fail.
Duk da haka, zai fi sauki sama da kasa su shude, da ko digo daya na attaura ya shude.
18 Whoever divorces his wife, and takes another, commits adultery; and whoever marries the divorced woman, commits adultery.
Duk wanda ya saki matansa ya auri wata ya aikata zina, kuma wanda ma ya auri sakakkiya ya aikata zina.
19 There was a certain rich man, that wore purple and fine linen, and feasted splendidly every day.
Akwai wani mai arziki, mai sa tufafi na alfarma masu tsada yana shagalin sa kowace rana.
20 There was also a poor man named Lazarus, covered with sores, that was laid at his gate,
Aka ajiye wani gajiyayye a kofarsa, mai suna liazaru wanda duk jikinsa miki ne,
21 and who was desirous to feed on the crumbs which fell from the rich man's table: yes, even the dogs came and licked his sores.
Shi kuwa yana marmarin ya koshi da barbashin da ke fadowa daga teburin mai arzikin nan har ma karnuka sukan zo suna lasar mikinsa.
22 It happened that the poor man died, and was conveyed by angels to Abraham's bosom: the rich man also died, and was buried.
Ana nan sai gajiyayyen nan ya mutu, malaiku kuma suka dauke shi suka kai shi wurin Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi,
23 And in hades, being in torments, he looked up, and saw Abraham afar off, and Lazarus in his bosom, (Hadēs g86)
yana cikin hades yana shan azaba, sai ya daga kai ya hangi Ibrahim daga nesa, da Li'azaru a kirjinsa. (Hadēs g86)
24 and cried, saying, Have pity on me, father Abraham, and send Lazarus to dip the tip of his finger in water, and cool my tongue; for I am tortured in this flame.
Sai ya yi kira ya ce, 'Baba Ibrahim, ka ji tausayi na, ka aiko Li'azaru ya tsoma dan yatsansa a ruwa ya sanyaya harshena, don azaba nake sha a cikin wannan wuta.'
25 Abraham answered, Son, remember that you, in your lifetime, received good things, and Lazarus received evil things; but now he is in joy, and you are in torments.
Amma Ibrahim ya ce, 'Yaro, ka tuna fa a zamanka na duniya ka sha duniyarka, ka kuma karba abubuwa masu kyau, amma Li'azaru kuma sai wahala. Amma yanzu dadi ake bashi a nan, kai kuwa kana shan azaba.
26 Besides, there lies a huge gulf between us and you, so that they who would pass hence to you, can not: neither can they pass to us, who would come thence.
Banda haka ma, akwai rami mai zurfi, domin wadanda suke son ketarewa zuwa wurinku kada su iya, kada kuma kowa ya ketaro zuwa wurinmu daga can.'
27 The other replied, I entreat you, then, father, to send him to my father's house;
Sai mai arziki ya ce, 'To ina rokonka, Baba Ibrahim, ka aike shi zuwa gidan mahaifina -
28 for I have five brothers, that he may admonish them, lest they also come into this place of torment.
domin ina da 'yan'uwa maza biyar, ya je ya yi masu gargadi kada su ma su zo wurin azaban nan.'
29 Abraham answered, They have Moses and the prophets, let them hear them.
Amma Ibrahim ya ce, 'Suna da Musa da annabawa; bari su saurare su.'
30 Nay, said he, father Abraham, but if one went to them from the dead, they would reform.
Sai mai arziki ya amsa, 'A'a, Baba Ibrahim, idan wani daga cikin matattu ya je wurinsu, zasu tuba.'
31 Abraham replied, if they hear not Moses and the prophets, neither will they be persuaded though one should arise from the dead.
Amma Ibrahim ya ce masa, 'In dai har basu saurari Musa da na annabawa ba, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su rinjayu ba.'”

< Luke 16 >