< Luke 1 >
1 Forasmuch as many have undertaken to compose a narrative of those things, which have been accomplished amongst us,
Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
2 as they, who were from the beginning, eye-witnesses, and afterwards ministers of the word, delivered them to us;
kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
3 I have also determined, having exactly traced everything from the first, to write a particular account for you, most excellent Theophilus;
Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
4 that you might know the certainty of those matters wherein you have been instructed.
Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
5 In the days of Herod, king of Judea, there was a priest named Zacharias, of the course of Abijah; and his wife, named Elizabeth, was of the daughters of Aaron.
A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
6 They were both righteous before God, blameless observers of all the Lord's commandments and ordinances.
Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
7 And they had no child, because Elizabeth was barren, and they were advanced in years.
Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
8 Now when he came to officiate as priest in the order of his course,
Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
9 it fell to him by lot, according to the custom of the priesthood, to offer incense in the sanctuary.
Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
10 And while the incense was burning, the whole congregation were praying without.
Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
11 Then there appeared to him an angel of the Lord, standing on the right side of the altar of incense.
A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
12 And Zacharias was discomposed at the sight, and in great terror.
Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
13 But the angel said to him, Fear not, Zacharias; for your prayer is heard, and Elizabeth your wife shall bear you a son, whom you shall name John.
Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
14 He shall be to you matter of joy and transport; and many shall rejoice because of his birth.
Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
15 For he shall be great before the Lord; he shall not drink wine nor any fermented liquor; but he shall be filled with the Holy Spirit, even from his mother's womb.
Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
16 And many of the sons of Israel he shall bring back to the Lord their God.
Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
17 Moreover, he shall go before him in the spirit and power of Elijah, to reconcile fathers to their children, and by the wisdom of the righteous, to render the disobedient a people well disposed for the Lord.
Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
18 And Zacharias said to the angel, How shall I know this: for I am old man, and my wife is advanced in years?
Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
19 The angel answering, said to him, I am Gabriel, who attend in the presence of God, and am sent to tell you this joyful news.
Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
20 But know that you shall be dumb, and shall not recover your speech, till the day when these things happen, because you have not believed my words, which shall be fulfilled in due time.
Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
21 Meanwhile the people waited for Zacharias, and wondered that he staid so long in the sanctuary.
Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
22 But when he came out, he could not speak to them; and they perceived that he had seen a vision in the sanctuary; for he made them understand by signs, and remained speechless.
Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
23 And when his days of officiating were expired, he returned home.
Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
24 Soon after, Elizabeth his wife conceived, and lived in retirement five months, and said,
Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
25 The Lord has done this for me, purposing now to deliver me from the reproach I lay under among men.
“Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
26 Now, in the sixth month, God sent Gabriel his angel, to Nazareth, a city of Galilee;
A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
27 to a virgin betrothed to a man called Joseph, of the house of David, and the virgin's name was Mary.
zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
28 When the angel entered, he said to her, Hail, favorite of heaven! the Lord be with you, happiest of women!
Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
29 At his appearance and words, she was perplexed, and revolved in her mind what this salutation could mean.
Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
30 And the angel said to her, Fear not, Mary, for you have found favor with God.
Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
31 And behold, you shall conceive and bear a son, whom you shall name Jesus.
Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
32 He shall be great, and shall be called the Son of the Highest. And the Lord God will give him the throne of David his Father.
Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
33 And he shall reign over the house of Jacob forever: his reign shall never end. (aiōn )
Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn )
34 Then said Mary to the angel, How shall this be, since I have no intercourse with man?
Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
35 The angel answering, said to her, The Holy Spirit will descend upon you, and the power of the Highest will overshadow you; therefore the holy progeny shall be called the Son of God.
Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
36 And lo! your cousin Elizabeth also has conceived, a son in her old age; and she who is called barren, is now in her sixth month;
Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
37 for nothing is impossible with God.
Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
38 And Mary said, Behold the handmaid of the Lord. Be it to me according to your word. Then the angel departed.
Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
39 In those days Mary set out, and traveled expeditiously into the hill country; to a city of Judah;
Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
40 where having entered the house of Zacharias, she saluted Elizabeth.
Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
41 As soon as Elizabeth heard Mary's salutation, the babe leaped in her womb; and Elizabeth was filled with the Holy Spirit,
Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
42 and cried with a loud voice, You are the most blessed of women, and blessed is the fruit of your womb.
Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
43 But how have I deserved this honor, to be visited by the mother of my Lord!
Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
44 for know, that as soon as the sound of your salutation reached my ears, the babe leaped in my womb for joy.
Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
45 And happy is she who believed that the things which the Lord has promised her, shall be performed.
Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
46 Then Mary said, My soul magnifies the Lord,
Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
47 and my spirit rejoices in God my Saviour;
kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
48 because he has not disdained the low condition of his handmaid; for henceforth, all posterity will pronounce me happy.
Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
49 For the Almighty, whose name is venerable, has done wonders for me.
Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
50 His mercy on them who fear him, extends to generations of generations.
Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
51 He displays the strength of his arm, and dispels the vain imaginations of the proud.
Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
52 He pulls down potentates from their thrones, and exalts the lowly.
Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
53 The needy he loads with benefits; but the rich he spoils of everything.
Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
54 He supports Israel his servant, ever inclined to mercy,
Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
55 (as he promised to our fathers) toward Abraham and his race. (aiōn )
(kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn )
56 And Mary, after staying with Elizabeth about three months, returned home.
Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
57 When the time for Elizabeth's delivery was come, she brought forth a son;
Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
58 and her neighbors and relations who heard that the Lord had shown her great kindness, rejoiced with her.
Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
59 And, on the eighth day, when they came to the circumcision of the child, they would have called him by his father's name, Zacharias.
Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
60 And his mother interposed, saying, No; but he shall be called John.
amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
61 They said to her, There is none of your kindred of that name.
Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
62 They, therefore, asked his father by signs, how he would have him called.
Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
63 He, having demanded a table-book, wrote upon it, His name is John, which surprised them all.
Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
64 And his mouth was opened directly, and his tongue loosed. And he spoke, praising God.
Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
65 Now all in the neighborhood were struck with awe; and the fame of these things spread throughout all the hill country of Judea.
Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
66 And all who heard these things, pondering them in their hearts, said, What will this child hereafter be? And the hand of the Lord was with him.
Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
67 Then Zacharias, his father, being filled with the Holy Spirit, prophesied, saying,
Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
68 Blessed be the Lord, the God of Israel, because he has visited and redeemed his people;
“Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
69 and has raised a Prince for our deliverance in the house of David his servant;
Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
70 (as anciently he promised by his holy prophets) (aiōn )
kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn )
71 for our deliverance from our enemies, and from the hands of all who hate us;
Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
72 in kindness to our forefathers, and remembrance of his holy institution;
Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 the oath which he swore to our father Abraham,
rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
74 to grant to us, that being rescued out of the hands of our enemies, we might serve him boldly,
Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
75 in piety and uprightness all our days.
a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
76 And you, child, shall be called a prophet of the Most High; for you shall go before the Lord, to prepare his way,
I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
77 by giving the knowledge of salvation to his people, in the remission of their sins,
domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
78 through the tender compassion of our God, who has caused a light to spring from on high to visit us,
Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
79 to enlighten those who abide in darkness and in the shades of death; to direct our feet into the way of peace.
domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
80 Meantime the child grew, and acquired strength of mind, and continued in the deserts, until the time when he made himself known to Israel.
Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.