< John 16 >
1 These things I tell you, that you may not be discouraged.
“Na fada maku wannan ne domin kada kuyi tuntube.
2 They will expel you from the synagogue; nay, the time is coming, when, whosoever kills you, will think he offers sacrifice to God.
Zasu fitar da ku daga majami'u. Amma, sa'a tana zuwa, wadda idan wani ya kasheku, zai yi zaton aikin Allah yake yi.
3 And these things they will do, because they know not the Father nor me.
Za suyi haka ne kuwa domin ba su san Uban ko ni ba.
4 Of these things I warn you now, that when the time shall come, you may remember that I mentioned them to you. I did not, indeed, mention them at the beginning, because I was with you myself.
Na fada maku wadannan abubuwa ne domin in lokacin da zasu faru yayi, ku tuna na fada maku.” Ban fada maku wadannan abubuwa ba tun da farko, domin ina tare da ku.
5 And now I go away to him who sent me; yet none of you ask me, Whither do you go?
Yanzu kuwa za ni wurin wanda ya aiko ni, duk da haka a cikinku, ba wanda ya tambaye ni, 'Ina za ka?'
6 But because of those things which I have foretold you, you are overwhelmed with grief.
Amma saboda na fada maku wadannan abubuwa, bakin ciki ya cika zuciyarku.
7 Nevertheless, I tell you the truth; it is for your good that I depart; for if I do not depart, the Advocate will not come to you; but if I go away, I will send him to you.
Amma ina gaya maku gaskiya: zai fi ye maku in na tafi. Domin in ban tafi ba, Mai Ta'aziyya ba zai zo gare ku ba, in kuwa na tafi, zan aiko shi gare ku.
8 And when he is come, he will convince the world concerning sin, and concerning righteousness, and concerning judgment:
Idan kuwa ya zo, Mai Ta'aziyyar zai fadarkar da duniya a kan zunubi, da adalci, da kuma hukunci.
9 concerning sin, because they believe not on me;
Game da zunubi, domin basu gaskata da ni ba,
10 concerning righteousness because I go to my Father, and you see me no longer;
Game da adalci, domin za ni wurin Uba, kuma ba za ku sake ganina ba,
11 concerning judgment, because the prince of this world is judged.
game da hukunci kuma, domin an yanke wa mai mulki duniyan nan hukunci.
12 I have many things still to tell you, but you can not yet bear them.
“Akwai abubuwa da yawa da zan gaya maku, amma ba za ku iya fahimta a yanzu ba.
13 But when the Spirit of Truth is come, he will conduct you into all the truth: for his words will not proceed from himself: but whatsoever he shall have heard, he will speak, and show you things to come.
Saboda haka, sa'adda Ruhu na gaskiya ya zo, zai bishe ku a cikin dukan gaskiyar, domin ba zai yi magana don kansa ba, sai dai duk abin da ya ji, shi zai fada, zai kuma sanar da ku al'amuran da zasu faru.
14 He will glorify me: for he will take of mine and communicate to you.
Zai daukaka ni, domin zai dauko abubuwa dake nawa ya sanar da ku.
15 Whatsoever is the Father's, is mine; therefore, I say that he will take of mine to communicate to you.
Duk abinda Uba yake da shi, nawa ne. Domin wannan ne nace zai dauko abubuwa da yake nawa ya sanar da ku.
16 A little while you shall not see me; a little while after, you shall see me; because I go to the Father.
“Bayan dan lokaci kadan, ba zaku kara ganina kuma ba. bayan dan lokaci kadan kuma, zaku gan ni.”
17 Some of the disciples said among themselves, What does he mean by this; a little while you shall not see me; a little while after, you shall see me; because I go to the Father?
Sai wadansu almajiransa sukace wa juna, “Me nene wannan da yake fadi mana, 'Bayan dan lokaci kadan ba zaku gan ni ba, bayan dan lokaci kadan kuma zaku gan ni?' da kuma, ' zan tafi wurin Uba'?”
18 What means this little while, of which he speaks? We do not comprehend it.
Saboda haka sukace, “Me nene wannan da yake fada, 'Bayan dan lokaci kadan'? Bamu san abinda yake fada mana ba.”
19 Jesus perceiving that they were desirous to ask him, said to them, Do you inquire among yourselves about this that I said, A little while you shall not see me; a little while after, you shall see me?
Yesu kuwa ya ga suna so su tambaye shi, sai ya ce masu, “Wato kuna tambayar juna ne abinda nake nufi da cewa, “Bayan dan lokaci kadan ba zaku gan ni ba, bayan dan lokaci kadan kuma zaku gan ni'?
20 Most assuredly, I say to you, you will weep and lament, but the world will rejoice: you will be sorrowful, but your sorrow shall be turned into joy.
Hakika, hakika, ina gaya maku, zaku yi kuka da makoki, amma duniya za ta yi farin ciki, zaku cika da bakin ciki, amma bakin cikinku zai koma farin ciki.
21 A woman in travail has sorrow, because her hour is come. But when her son is born, she remembers her anguish no longer; for joy that she has brought a man into the world.
Mace takan ji zafi lokacin da take nakuda don lokacin haihuwa ya zo. Amma da zarar ta haifi jinjirin nan, ba ta kara tunawa da zafin, domin ta na fariciki an haifi mutum a duniya.
22 So, you, at present, are in grief; but I will visit you again, and your hearts shall be joyful, and none shall rob you of your joy.
To yanzu dai kuna bakin ciki, amma zan sake ganinku, kuma ba wanda zai iya kwace maku wannan farin ciki.
23 On that day, you will put no questions to me. Most assuredly, I say to you, whatsoever you shall ask the Father, in my name, he will give you.
A rannan, ba zaku tambaye ni komai ba. Hakika hakika, ina gaya maku, komai kuka roki Uba a cikin sunana zai ba ku shi.
24 Hitherto you have asked nothing in my name; ask, and you shall receive, that your joy may be complete.
Harwa yau, ba ku roki komai cikin sunana ba. Ku roka, zaku karba, domin farin cikin ku ya zama cikakke.”
25 These things I have spoken to you in figures: the time approaches when I shall no more discourse to you in figures, but instruct you plainly concerning the Father.
“Na fada maku wadannan abubuwa cikin karin magana. Amma sa'a tana zuwa da ba zan kara fada maku komai ba cikin karin magana, amaimakon haka zan gaya maku komai a sarari game da Uba.
26 The you will ask in my name, and I say not, that I will entreat the Father for you:
A ranar nan, zaku yi roko a cikin sunana kuma bance maku zan yi addu'a ga Uba a madadinku ba,
27 for the Father himself loves you, because you have loved me, and believed that I came from God.
domin Uba da kansa yana kaunarku, domin kun kaunace ni, kun kuma gaskata daga wurin Uban na fito.
28 From the presence of the Father I cam into the world. Again, I leave the world, and return to the Father.
Daga wurin Uban na fito, kuma na shigo duniya. Har wa yau, kuma zan bar duniya in koma wurin Uba.”
29 His disciples replied, Now, indeed, you speak plainly, and without a figure.
Almajiransa sukace, duba, “Yanzu kake magana a sarari, ba cikin karin magana ba!
30 Now we are convinced that you know all things, and need not that any should put questions to you. By this we believe that you came forth from God.
Yanzu mun sani ka san komai, ba sai wani ya tambaye ka ba. Ta haka muka gaskata daga wurin Allah ka fito.”
31 Jesus answered, Do you now believe?
Yesu ya amsa masu yace, “Ashe, yanzu kun gaskata?
32 Behold, the time comes, or rather is come, when you shall disperse, every one to his own, and shall leave me alone; yet I am not alone, because the Father is with me.
Duba, sa'a na zuwa, I, sa'ar ta yi, da za a warwatsa ku, kowa ya koma gidansa, kuma ku bar ni ni kadai. Duk da haka kuwa ba ni kadai nake ba, domin Ubana yana tare da ni.
33 These things I have spoken to you, that in me you may have peace. In the world you will have tribulation. But take courage! I have overcome the world.
Na fada maku wannan ne domin a ciki na ku sami salama. A duniya kuna shan tsanani, amma ku karfafa: na yi nasara da duniya,”