< Acts 2 >

1 And when the day of Pentecost was fully come, they were all unanimously assembled in the same place:
Da ranar Fentikos ta zo, dukansu suna tare wuri daya.
2 and, on a sudden, there was a sound from heaven, as of a rushing violent wind; and it filled all the house where they were sitting.
Nan da nan sai ga wata kara daga sama kamar ta babbar iska, kuma ta sauko ta cika duka gidan inda suke zaune.
3 And there appeared to them tongues resembling fire, distinctly separated, and it rested upon each of them,
Sai ga wasu harsuna kamar na wuta sun bayyana a garesu aka rarraba su, kuma suka zauna bisa kowannensu.
4 and they were all filled with the Holy Spirit, and began to speak in other languages, as the Spirit gave them utterance.
Dukansu suka cika da Ruhu Mai Tsarki suka fara magana da wadansu harsuna, yadda Ruhu ya ba su iko su yi magana.
5 Now there were sojourning in Jerusalem pious men; Jews from every nation under heaven;
A lokacin akwai Yahudawa dake zaune a Urushalima, mutanen Allah, daga kowace kasa karkashin sama.
6 and when this report came abroad, the multitude assembled, and were confounded; for every one heard them speaking in his own dialect.
Da suka ji wannan kara jama'a duk suka taru suka rude saboda kowannensu ya ji suna magana da harshensa.
7 And they were all astonished, and wondered, saying one to another, Behold! are not all these that speak, Galileans?
Suka yi mamaki matuka; suka ce, ''Lallai, wadannan duka ba Galiliyawa ba ne?
8 And how do we every one hear in his own native language:
Yaya mu ke jinsu duka, kowannensu na magana a cikin harshen da aka haife mu?
9 Parthians, and Medes, and Elamites, and those that inhabit Mesopotamia, and Judea, and Cappadocia, Pontus, and Asia,
Fisiyawa da Mediyawa da Elimawa, da Yahudawa da Kafadokiya, cikin Fontus da Asiya,
10 Phrygia, and Pamphilia, Egypt, and the parts of Africa which are about Cyrene: Roman strangers, also, both Jews and proselytes;
cikin Firgia da Bamfiliya, cikin Masar da yankunan Libiya ta wajen Sur, da baki daga Roma,
11 Cretes, and Arabians; we hear them speaking in our own tongues the wonderful works of God!
Yahudawa da tubabbun cikin Yahudanci, Kiretawa da Larabawa, duk munji su suna fadi a harshenmu game da manyan ayyukan Allah.''
12 And they were all in amazement and perplexity, and said one to another, What can this mean?
Dukansu suka yi mamaki suka rikice; suka ce da junansu, ''Menene ma'anar wannan?''
13 But others, mocking, said, Surely these men are filled with sweet wine.
Amma wasu suka yi ba'a suka ce, ''Sun bugu ne da sabon ruwan inabi.''
14 But, Peter, standing up with the eleven, raised his voice, and said to them--Jews, and all you that sojourn in Jerusalem, let this be known to you, and attend to my words;
Amma Bitrus ya tashi tare da sha dayan, ya daga murya ya ce da su, ''Mutanen Yahuda da dukanku dake zaune a Urushalima, bari ku san wannan; ku saurari maganata.
15 for these men are not drunk, as you suppose, since it is but the third hour of the day:
Domin wadannan mutanen ba buguwa suka yi ba yadda kuke zato, domin yanzu karfe tara ne na safe kawai.
16 but this is that which was spoken by the Prophet Joel,
Amma wannan shine abinda aka fada ta wurin annabi Yowel.
17 "And it shall come to pass in the last days, says God, I will pour out a portion of my Spirit upon all flesh; and your sons and daughters shall prophesy; and your young men shall see visions, and your old men shall dream dreams.
Allah ya ce, 'Haka zai kasance a kwanakin karshe, zan zubo Ruhuna a kan dukan mutane, 'ya'yanku maza da mata za su yi anabci, kuma samarinku za su ga wahayoyi, kuma tsofaffinku za su yi mafarkai.
18 Yes, in those days I will pour out of my Spirit upon my servants, and upon my handmaids; and they shall prophesy;
Haka kuma a bisa bayi na maza da mata, a kwanakin nan zan zubo da Ruhuna, kuma za su yi anabci.
19 and I will give prodigies in heaven above, and signs in the earth beneath; blood and fire, and a cloud of smoke:
Zan nuna al'ajibai a sararin sama da kuma alamu a bisa duniya, jini da wuta, da girgije.
20 the sun shall be turned into darkness, and the moon into blood, before that great and illustrious day of the Lord come.
Rana zata juya ta koma duhu kuma wata ya koma jini, kafin Babbar ranan nan ta Ubangiji ta zo.
21 And it shall come to pass, that whosoever shall invoke the name of the Lord shall be saved."
Zai kuma zama dukan wanda ya kira ga sunan Ubangiji zai sami ceto.
22 Israelites, hear these words: Jesus, the Nazarene, a man recommended to you by God, by powerful operations, and wonders, and signs, which God wrought by him in the midst of you, (as you yourselves also know, )
Mutanen Isra'ila, ku saurari wadannan magana. Yesu Banazare, mutumin da Allah ya tabbatar da shi gareku ta wurin manyan ayyuka da ban mamaki da alamu da Allah ya yi ta wurinsa a tsakiyarku, kamar yadda ku da kanku kuka sani.
23 him you have apprehended, being given up by the declared counsel and foreknowledge of God, and by the hands of sinners have crucified and slain:
Saboda tabbataccen shiri da riga sani na Allah, aka bayar dashi, ku kuma, ta hannun mutane 'yan tawaye, kuka gicciye shi kuma kuka kashe shi.
24 whom God raised up, having loosed the pains of death, as it was impossible that he should be held under it.
Wanda Allah ya tayar, bayan ya cire zafin mutuwa daga gareshi, saboda ba zai yiwu ba ta rike shi.
25 For David says, concerning him, "I have regarded the Lord as always before me; because he is at my right hand, that I might not be moved:
Gama, game da shi, 'Ina ganin Ubangiji a gabana ko yaushe, domin yana gefen hannun damana saboda kada in firgita.
26 for this reason my heart is glad, and my tongue exults; moreover, too, my flesh shall rest in hope
Saboda haka zuciyata na farin ciki harshena yana yin murna. Kuma, jikina zai zauna gabagadi.
27 that thou wilt not leave my soul in the unseen world, neither wilt thou permit thy Holy One to see corruption. (Hadēs g86)
Gama ba za ka watsar da raina a lahira ba, ba kuwa za ka bar Mai Tsarkinka ya ga ruba ba. (Hadēs g86)
28 Thou hast made me to know the ways of life; thou wilt make me full of joy with thy countenance."
Ka bayyana mani hanyar rai; da fuskarka zaka cika ni da farin ciki.
29 Brethren, permit me to speak freely to you concerning the patriarch David; the he is both dead and buried, and his sepulcher is among us to this day;
'Yan'uwa, zan yi magana da ku gabagadi game da baba Dauda: ya mutu kuma aka bizne shi, kuma kabarinsa na nan tare da mu har yau.
30 therefore, being a prophet, and knowing that God had sworn to him with an oath, that of the fruit of his loins he would raise up the Messiah to sit on his throne;
Domin haka, don shi annabi ne kuma ya san Allah ya yi masa alkawari da rantsuwa cewa daga cikin zuriyarsa zai sanya wani bisa kursiyinsa.
31 he, foreseeing this, spoke of the resurrection of the Messiah, that his soul should not be left in the unseen world, nor his flesh see corruption. (Hadēs g86)
Ya hango wannan al'amari kuma ya yi magana game da tashin Almasihu, 'Ba ayi watsi da shi ba a lahira, kuma jikinsa bai ga rubewa ba.' (Hadēs g86)
32 This Jesus, God has raised up, of which all we are witnesses:
Wannan Yesun - Allah ya tashe shi, wanda dukanmu shaidu ne.
33 being exalted, therefore, to the right hand of God, and having received the promise of the Holy Spirit from the Father, he has shed forth this, which you see and hear.
Saboda haka yadda aka tashe shi zuwa hannun dama na Allah kuma ya karbi alkawarin Ruhu Mai Tsarki daga wurin Uba, shine ya zubo mana wannan da kuke gani kuma kuke ji.
34 For David is not ascended into heaven, but he says, "The Lord said to my Lord, Sit thou at my right hand,
Dauda bai hau zuwa sama ba, amma ya ce, ''Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna hannun dama na,
35 till I make thy foes thy footstool.
har sai na maida makiyanka abin takawar sawunka.'''
36 Let, therefore, all the house of Israel assuredly know, that God has made this Jesus, whom you have crucified, Lord and Messiah.
Saboda haka, bari gidan Isra'ila su sani tabbas wannan Yesun wanda kuka gicciye, Allah ya maishe shi Ubangiji da kuma Almasihu.
37 Now, when they heard these things, they were pierced to the heart, and said to Peter, and the rest of the Apostles, Brethren, what shall we do?
Da suka ji haka sai suka soku a zukatansu, suka cewa Bitrus da sauran manzanni, '''Yan'uwa me za mu yi?''
38 And Peter said to them, Reform, and be each of you immersed in the name of Jesus Christ, in order to the remission of sins, and you shall receive the gift of the Holy Spirit.
Sai Bitrus ya ce masu, ''Ku tuba ayi wa kowannenku baftisma, cikin sunan Yesu Almasihu domin gafarar zunubanku, kuma za ku karbi baiwar Ruhu Mai Tsarki.
39 For the promise is to you, and to your children, and to all that are afar off; as many as the Lord our God shall call.
Domin alkawarin a gareku ne da 'ya'yanku da duk wadanda ke nesa, dukan iyakar mutanen da Ubangiji Allahnmu zai kira.''
40 And with many other words he testified, and exhorted, saying, Save yourselves from this perverse generation.
Da maganganu da yawa ya ba da shaida kuma ya karfafa su; ya ce, ''Ku ceci kan ku daga wannan muguwar tsara.''
41 They, therefore, who received his word with readiness, were immersed: and there were added to the disciples that very day, about three thousand souls.
Sai suka karbi maganar sa kuma aka yi ma su baftisma, a wannan rana kuma aka sami karin rayuka wajen dubu uku.
42 And they continued steadfast in the teaching, in the fellowship, in the breaking of the load, and in the prayers of the Apostles.
Su ka cigaba cikin koyarwar manzanni da zumunta, cikin kakkaryawar gurasa da kuma cikin addu'o'i.
43 Fear also fell upon every soul, and many miracles and signs were wrought by the Apostles.
Tsoro ya sauko bisa kowane rai, kuma aka yi abubuwan ban mamaki da alamu da yawa ta wurin manzannin.
44 And all that believed were together, and had all things in common.
Duka wadanda suka ba da gaskiya suna tare kuma komai nasu na kowanensu ne,
45 They also sold their possessions and effects, and distributed them to every one according to his necessity.
kuma suka saida kadarorinsu da mallakarsu kuma suka rarrabawa kowa, bisa ga irin bukatar da kowannensu yake da ita.
46 Moreover, they continued unanimously in the temple every day; and breaking bread from house to house, they partook of their food with joy and simplicity of heart,
A kowace rana suka cigaba tare da nufi daya a cikin haikali, suna kakkarya gurasa a gidaje, kuma suna raba abinci tsakaninsu cikin farin ciki da tawali'u a zuciya;
47 praising God, having favor with all the people: and the Lord daily added the saved to the congregation.
Suna yabon Allah kuma suna da tagomashi a gaban dukan mutane. Ubangiji kuma kullum yana kara masu wadanda suke samun ceto.

< Acts 2 >