< 2 Timothy 1 >

1 Paul, an Apostle of Jesus Christ, by the will of God, on account of the promise of life, which is by Christ Jesus;
Bulus, manzon Almasihu Yesu ta wurin nufin Allah, bisa ga alkawarin rai da ke cikin Almasihu Yesu,
2 to Timothy, my beloved son: Favor, mercy, and peace, from God the Father, and from Christ Jesus our Lord.
zuwa ga Timoti, kaunataccen da: Alheri, jinkai, da salama daga Allah Uba da Almasihu Yesu Ubangijinmu.
3 I give thanks to God, (whom from my forefathers I serve with a pure conscience, ) that I have unceasing remembrance of you in my prayers night and day;
Na gode wa Allah, wanda na ke bautawa tun daga kakannina, da lamiri mai tsabta, sa'adda na ke tuna wa da kai cikin addu'o'ina koyaushe (dare da rana).
4 remembering your tears, I greatly desire to see you, that I may be filled with joy:
Sa'adda na tuna da hawayenka, na yi marmarin ganinka, saboda in cika da farin ciki.
5 calling to remembrance also the unfeigned faith which is in you, which dwelt first in your grandmother Lois, and in your mother Eunice, and I am persuaded that it dwells in you also.
An tunashshe ni game da sahihiyar bangaskiyarka, wadda ta samo asali daga kakarka Loyis da mahaifiyarka Afiniki. Na kuma tabbata ta na zaune a cikinka.
6 For which cause I put you in mind to stir up the spiritual gift of God, which is in you through the imposition of my hands.
Wannan shine dalilin da ni ke tunashshe ka cewa ka sake rura baiwar Allah da ke cikinka wadda ka samu sa'adda na dibiya maka hannuwana.
7 For God has not given us a spirit of cowardice; but of power, and of love, and of self-government.
Domin Allah bai ba mu ruhun tsoro ba, amma na iko da kauna da kamun kai.
8 Wherefore, be not ashamed of the testimony of our Lord, nor of me his prisoner; but jointly suffer evil for the gospel, according to the power of God;
Saboda haka kada ka ji kunyar shaida ga me da Ubangijinmu, ko ni, Bulus, daurarrensa. Maimakon haka, ka zama a shirye ka sha wahala domin bishara bisa ga ikon Allah.
9 who has saved us, and called us with a holy calling, --not on account of our works; but on account of his own purpose and favor, which was given us through Christ Jesus, before the times of the ages, (aiōnios g166)
Allah ne ya cecemu kuma ya kira mu da kira mai tsarki. Ya yi wannan, ba ta wurin ayyukanmu ba, amma ta wurin shirinsa da alherinsa. Ya ba mu wadannan abubuwan a cikin Almasihu Yesu kafin farkon zamanai. (aiōnios g166)
10 and is now manifest by the appearing of our Saviour Jesus Christ; who has, indeed, vanquished death, and brought life and incorruptibility to light by the gospel:
Amma yanzu an bayyana ceton Allah ta wurin bayyanuwar mai cetonmu Almasihu Yesu. Almasihu ne ya kawo karshen mutuwa ya kuma kawo rai marar karshe da ya bayyana ta wurin bishara.
11 of which I am appointed a herald, and an Apostle, and a teacher of the Gentiles:
Domin wannan, an zabe ni mai wa'azi, manzo da mallami zuwa ga al'ummai.
12 for which cause I also suffer these things. Nevertheless, I am not ashamed; for I know in whom I have believed, and I am persuaded that he is able to preserve what I have committed in trust to him, till that day.
Domin wannan dalili na ke shan wahalar wadannan abubuwa. Amma ban ji kunya ba, domin na san shi, wanda na gaskanta. Na sakankance zai iya adana abinda na mika masa har zuwa ranan nan.
13 The form of wholesome words, which you have heard from me, hold fast, with the faith and love which are in Christ Jesus.
Ka adana misalin amintattun sakwanni da ka ji daga gare ni, ta wurin bangaskiya da kauna da ke cikin Almasihu Yesu.
14 The good deposit guard by the Holy Spirit, who dwells in us.
Abu mai kyau da Allah ya danka maka, ka tsare shi ta wurin Ruhu Mai Tsarki, da ke zaune a cikinmu.
15 You know this, that all they who are in Asia have turned me off; of whom are Phygellus and Hermogenes.
Ka dai sani, dukkan wadanda su ke zama a Asiya sun juya mani baya. A cikin kungiyar akwai Fijalas da Harmajanas.
16 May the Lord grant mercy to the family of Onesiphorus; for he often refreshed me, and was not ashamed of my chain:
Bari Ubangiji ya yi wa iyalin Onisifaras jinkai, domin ya na yawan yi mani hidima, kuma ba ya jin kunyar sarkata.
17 but being in Rome, he sought me out very diligently, and found me.
Maimakon haka, sa'adda ya ke a Roma, ya neme ni da kokarin gaske, ya kuma same ni.
18 May the Lord grant him to find mercy from the Lord in that day! And how many services he rendered to me in Ephesus, you well know.
Bari Ubangiji ya sa, ya sami jinkai daga gare shi a wannan rana. Dukkan hanyoyin da ya taimake ni a kasar Afisa, kun sani sarai.

< 2 Timothy 1 >