< 2 Peter 2 >

1 But there were also false prophets among the people, even as there will be false teachers among you; who will privately introduce destructive sects, denying even the Lord who bought them, bringing on themselves swift destruction.
Annabawan karya sun zo ga mutane, hakannan kuma malaman karya suma sun zo. A asirce za su zo maku da karkatacciyar koyarwa mai hallakarwa, su kuma yi musun sanin Ubangiji da ya fanshe su. Su na jawowa kansu hallaka da sauri.
2 And many will follow their lewd practices, on account of whom, they way of truth will be evil spoken of.
Da yawa za su bi gurbinsu, kuma ta wurinsu za a sabawa sahihiyar gaskiya.
3 And through covetousness, they will make merchandise of you, by fictitious tales: to whom the punishment threatened of old lingers not, and their destruction slumbers not.
Ta wurin hadama za su ribace ku ta wurin maganganunsu na yaudara. Hallakarsu ba za ta yi jinkiri ba; hukuncinsu na nan tafe.
4 For God, indeed, did not spare the angels who sinned, but with chains of darkness confining them in Tartarus, delivered them over to be kept for judgment; (Tartaroō g5020)
Allah bai kebe mala'ikkun da suka yi zunubi ba. Maimakon haka ya tura su a cikin bakin duhun jahannama daure da sarkoki, har ya zuwa ranar shari'a. (Tartaroō g5020)
5 and did not spare the old world, but saved Noah, the eighth, a proclaimer of righteousness, when he brought the flood upon the world of the ungodly;
Hakan nan kuma bai kebe duniya ta zamanin da ba. Maimakon haka, ya kebe Nuhu, wanda yake wa'azin adalci, tare da mutane bakwai, lokacin da ya kawo ambaliyar ruwan Tsufana a fuskar duniyar marasa bin Allah.
6 and having reduced to ashes the cities of Sodom and Gomorrah, punished them with an overthrow, making them an example to those who should afterward live ungodly:
Sa'annan Allah ya kone biranen Sadoma da Gomrata da wuta ya maishe su toka, wannan ya zama misalin abin da zai faru da marasa ibada.
7 and rescued righteous Lot, exceedingly grieved by the lewd behavior of the lawless:
Amma ga adalinnan Lutu, wanda ya zaku a ransa ta wurin miyagun halayen mutanen, Ubangiji kuwa ya cece shi.
8 (for; --that righteous man, dwelling among them, by the sight and report of their unlawful deeds, tormented his righteous soul from day to day; )
Ga wannan mutum mai adalci, wanda yayi zama a cikinsu kowace rana ransa na baci, domin abin da yake gani yake kuma ji.
9 the Lord knows how to rescue the godly out of temptation, and to reserve the unrighteous to a day of judgment to be punished;
Saboda haka Allah ya san yadda zai ceci masu adalci daga gwaji, da yadda kuma zai kama masu rashin adalci da hukunci a ranar shari'a.
10 but especially those who go after the flesh in the lust of uncleanness, and who despise government: being audacious, self-willed, who fear not to revile dignitaries;
Wannan kuwa musamman gaskiya ce ga wadanda suka ci gaba da ayyuka na jiki suka kuma raina masu mulki. Suna da taurin kai da kuma yin ganin dama. Ba sa tsoron sabo ga wadanda aka daukaka.
11 whereas, angels, who are greater in strength and power, do not bring a reviling accusation against them before the Lord.
Ko da shike mala'iku suna da karfi da iko fiye da su, amma basu kawo karar batanci a kansu a gaban Ubangiji ba.
12 But these, as natural, irrational animals, made for capture and destruction, speaking evil of matters which they do not understand, shall be utterly destroyed by their own corruptions;
Amma wadannan dabbobi marassa tunani an yi su ne musamman domin a kama a yanka. Suna sabawa abin da ba su sani ba. Zasu halaka.
13 receiving the due reward of unrighteousness. These delight to spend the day in luxurious festivity: they are spots and blemishes, reveling in their deceits when they feast with you;
Za su sami sakamakon mugun aikinsu. Suna tunanin yin nishadi da rana abin annashuwa ne. Su kan su tababbu ne. Suna jin dadin ayyukansu na yaudara yayin da suke liyafa tare da ku.
14 having eyes full of the adulteress, incessantly sinning, alluring unstable souls; having a heart exercised with insatiable desires; an accursed progeny:
Suna da idanun sha'awace sha'awacen mata mazinata; ba sa koshi da aikata zunubi. Suna rinjayar wandanda ba su da tsayayyan hankali zuwa ga munanan ayyuka, kuma sun kafa zukatansu ga hadama, su 'ya'yan la'ana ne!
15 having forsaken the right path, they have wandered, following in the way of Balaam, the son of Bosor, who loved the wages of iniquity,
Sun bar bin hanyar gaskiya. Sun bijire kuma sun bi hanyar Bal'amu dan Be'or wanda yake kaunar ribar rashin adalci.
16 and was convicted of his transgression; the dumb brute, speaking with man's voice, reprimanded the madness of the prophet.
Amma ya karbi tsautawa domin zunubinsa. Jaki ma da baya magana ya tsauta wa haukan annabin da muryar dan adam.
17 These are wells without water, clouds driven by a tempest; for whom the blackness of darkness is reserved forever:
Wadannan mutane suna kamar mabulbullai da babu ruwa. suna nan kamar gizagizai da iska ke korawa. Duhu mai tsanani yana jiransu.
18 for, speaking great swelling words of falsehood, they allure by the lusts of the flesh, even by lasciviousness, those who have actually fled away from them who are living in error.
Su masu babatu ne da girman kai. suna yadaurar mutane ta wurin sha'awowin jiki. Suna yaudarar mutane da suke kokarin su tsere daga wadanda suke rayuwa cikin kuskure.
19 They promise them liberty, whilst they themselves are slaves of corruption: for every one is enslaved by that which overcomes him.
Suna masu alkawarin yanci, amma su da kan su bayi ne ga zunubi. Domin mutum bawa ne ga duk abinda ya rinjaye shi.
20 Now, if, having fled away from the pollutions of the world, through the knowledge of the Lord and Saviour Jesus Christ, and being again entangled, they are overcome by them; their last condition is worse than the first.
Duk wanda ya kubuta daga shashanci na duniya ta wurin sanin Ubangiji da mai Ceto Yesu Almasihu, sa'annan ya koma cikin shashaci, yanayinsu na karshe ya zama da muni fiye da na farkon.
21 Therefore, it has been better for them not to have known the way of righteousness, than having known it, turn away from the holy commandment delivered to them.
Da ma zai fi masu kada su san hanyar adalci da su san ta amma sa'annan su juya daga ka'ida mai tsarki wanda aka damka masu.
22 But the saying of the true proverb has happened to them: "The dog is returned to his own vomit; and the washed hog, to its wallowing in the mire."
Wannan karin magana ya zama gaskiya a kan su: “Kare ya dawo yana lashe amansa. Aladen da akayi masa wanka ya koma cikin tabo.”

< 2 Peter 2 >