< 1 Corinthians 4 >

1 So, then, let a man consider us as servants only of Christ, and stewards of the secrets of God.
Ga yadda za ku dauke mu, kamar bayin Almasihu da kuma masu rikon asiran Allah.
2 Now, it is required in stewards, that every one be found faithful.
Hade da wannan, ana bukatar wakilai su zama amintattu.
3 Therefore, to me it is a very small matter that I be condemned by you, or by human judgment, seeing I do not condemn myself.
Amma a gare ni, karamin abu ne ku yi mani shari'a, ko a wata kotu irin ta mutane. Gama bani yi wa kaina shari'a.
4 For I am conscious to myself of no fault. However, I am not by this justified; but he who judges me is the Lord.
Ban sani ko akwai wani zargi a kaina ba, amma wannan bai nuna cewa bani da laifi ba. Ubangiji ne mai yi mani shari'a.
5 Wherefore, do not, before the time, pass any judgment, till the Lord come; who both will bring to light the hidden things of darkness, and lay open the counsels of the hearts; and then praise shall be to every one from God.
Sabili da haka, kada ku yanke shari'a kafin lokaci, kafin Ubangiji ya dawo. Zai bayyana dukkan boyayyun ayyuka na duhu, ya kuma tona nufe-nufen zuciya. San nan kowa zai samu yabonsa daga wurin Allah.
6 Now, these things, brethren, I have figuratively applied to myself, and Apollos, for your sakes, that by us you may learn not to esteem teachers above what has been written, that no one of you may, on account of one teacher, be puffed up against another.
Yan'uwa, ina dora wadannan ka'idoji a kaina da Afollos domin ku, yadda ta wurin mu za ku koyi ma'anar maganar nan cewa, “kada ku zarce abin da aka rubuta.” Ya zama haka domin kada waninku ya kumbura yana nuna fifiko ga wani akan wani.
7 Besides, who makes you to differ? For what have you which you did not receive? And now, if you did receive it, why do you boast as not receiving it?
Gama wa yaga bambanci tsakanin ku da wasu? Me kuke da shi da ba kyauta kuka karba ba? Idan kyauta kuka karba, don me kuke fahariya kamar ba haka ba ne?
8 Now you are filled! now you are become rich! you have reigned without it! and I wish, indeed, you had reigned, that we also might reign with you.
Kun rigaya kun sami dukkan abubuwan da kuke bukata! Kun rigaya kun zama mawadata! Kun rigaya kun fara mulki- kuma ba tare da mu ba! Hakika, marmarina shine ku yi mulki, domin mu yi mulki tare da ku.
9 For I think that God has set forth us, the Apostles, last, as persons appointed to death; because we are made a spectacle to the world, even to angels, and to men.
A tunanina, mu manzanni, Allah ya sa mu a jerin karshe kamar mutanen da aka zartar wa hukuncin mutuwa. Mun zama abin kallo ga duniya, ga mala'iku, ga mutane kuma.
10 We are fools on account of Christ; but you are wise in Christ: we are weak, but you are strong: you are honored, but we are despised.
Mun zama marasa wayo sabili da Almasihu, amma ku masu hikima ne a cikin Almasihu. Mu raunana ne, amma ku masu karfi ne. Ana ganin mu marasa daraja, ku kuwa masu daraja.
11 To the present hour we both hunger and thirst, and are naked, and are buffeted, and have no certain dwelling place,
Har zuwa wannan sa'a, muna masu yunwa da kishi, marasa tufafi masu kyau, mun sha kazamin duka, kuma mun zama marasa gidaje.
12 and labor, working with our own hands: when reviled, we bless: when persecuted, we bear:
Mun yi fama sosai, muna aiki da hanuwanmu. Sa'adda an aibata mu, muna sa albarka. Sa'adda an tsananta mana, muna jurewa.
13 when defamed, we beseech: when we are become as the purgations of the world, the filth of all things until now.
Sa'adda an zage mu, muna magana da nasiha. Mun zama, kuma har yanzu an dauke mu a matsayin kayan shara na duniya da abubuwa mafi kazamta duka.
14 I write not these things to shame you; but, as my beloved children, I instruct you.
Ban rubuta wadannan abubuwa domin in kunyata ku ba, amma domin in yi maku gyara kamar kaunatattun yayana.
15 For, though you have ten thousand teachers in Christ, yet you have not many fathers; for, to Christ Jesus, through the gospel, I have begotten you.
Ko da kuna da masu riko dubu goma a cikin Almasihu, ba ku da ubanni da yawa. Gama ni na zama ubanku cikin Almasihu Yesu ta wurin bishara.
16 Wherefore, I beseech you, be imitators of me.
Don haka, ina kira gare ku da ku zama masu koyi da ni.
17 For this purpose I have sent to you Timothy, who is my beloved son, and faithful in the Lord: he will put you in mind of my ways, which are in Christ, even as I teach everywhere, in every congregation.
Shiyasa na aiko Timoti wurin ku, kaunatacce da amintaccen dana cikin Ubangiji. Zai tunashe ku hanyoyina cikin Almasihu, kamar yadda nake koyar da su ko'ina da kowace Ikilisiya.
18 Now, some are puffed up, as if I were not coming to you.
Amma yanzu, wadansun ku sun zama masu fahariya, suna yin kamar ba zan zo wurinku ba.
19 But I will come to you soon, if the Lord will, and shall know, not the speech of them who are puffed up, but the power.
Amma zan zo gare ku ba da dadewa ba, idan Ubangiji ya nufa. Sannan zan san fiye da maganar masu fahariya, amma kuma zan ga ikonsu.
20 For the Reign of God is not in word, but in power.
Gama Mulkin Allah ba magana kadai ya kunsa ba, amma ya kunshi iko.
21 What do you incline? Shall I come to you with a rod, or in love, and in the spirit of meekness?
Me kuke so? In zo wurin ku da sanda ne ko kuwa da kauna da ruhun nasiha?

< 1 Corinthians 4 >