< Zechariah 9 >
1 The burden of a word of YHWH against the land of Hadrach, and Demmeseh—his place of rest: (When to YHWH [is] the eye of man, And of all the tribes of Israel).
Annabci. Maganar Ubangiji tana gāba da ƙasar Hadrak za tă kuma sauko a kan Damaskus, gama idanun dukan mutane da na kabilan Isra’ila suna a kan Ubangiji,
2 And also Hamath borders thereon, Tyre and Sidon, for—very wise!
da kuma a kan Hamat ita ma, wadda ta yi iyaka da ita, da kuma a kan Taya da Sidon, ko da yake suna da hikima ƙwarai.
3 And Tyre builds a bulwark for herself, And heaps silver as dust, And gold as mire of out-places.
Taya ta gina wa kanta mafaka mai ƙarfi; ta tara azurfa kamar ƙasa, zinariya kuma kamar tarin shara a tituna.
4 Behold, the Lord dispossesses her, And He has struck her force in the sea, And she is consumed with fire.
Amma Ubangiji zai karɓe mallakarta, zai hallaka ikonta da take da shi a kan teku, wuta kuma za tă cinye ta.
5 Ashkelon sees and fears, Also Gaza, and she is exceedingly pained, Also Ekron—for her expectation dried up, And a king has perished from Gaza, And Ashkelon does not remain,
Ashkelon za tă ga haka ta ji tsoro; Gaza za tă yi birgima cikin azaba, haka Ekron ma, gama za tă fid da zuciya. Gaza za tă rasa sarkinta za a kuma gudu a bar Ashkelon.
6 “And a foreigner has dwelt in Ashdod, And I have cut off the excellence of the Philistines.
Baƙi za su mallaki Ashdod, kuma zan kawar da girman kan Filistiyawa.
7 And turned aside his blood from his mouth, His abominations from between his teeth, And he has remained, even he, to our God, And he has been as a leader in Judah, And Ekron as a Jebusite.
Zan kawar da jini daga bakinsu, zan kuma cire abincin da aka haramta daga tsakanin haƙoransu. Waɗanda za a bari za su zama na Allahnmu, su kuma zama shugabanni a Yahuda, Ekron kuma za tă zama kamar Yebusiyawa.
8 And I have pitched a camp for My house, Because of the passer through, and of the returner, And an exactor does not pass through against them again, For now, I have seen with My eyes.
Amma zan kāre gidana daga sojoji masu kai da kawowa. Azzalumi ba zai ƙara cin mutanena da yaƙi ba, gama yanzu ina tsaro.
9 Rejoice exceedingly, O daughter of Zion, Shout, O daughter of Jerusalem, Behold, your King comes to you, Righteous and having salvation, Afflicted—and riding on a donkey, And on a colt—a son of female donkeys.
Ki yi murna ƙwarai, ya Diyar Urushalima! Ki yi sowa, Diyar Urushalima! Duba, ga sarkinki yana zuwa wurinki, mai adalci yana kuma da ceto, mai tawali’u yana kuma hawan jaki, yana a kan ɗan aholaki, a kan’yar jaka.
10 And I have cut off the chariot from Ephraim, And the horse from Jerusalem, Indeed, the bow of battle has been cut off, And He has spoken peace to nations, And His rule [is] from sea to sea, And from the river to the ends of the earth.
Zan ƙwace kekunan yaƙi daga Efraim, da kuma dawakan yaƙi daga Urushalima, za a kuma karya bakan yaƙi. Zai yi shelar salama ga al’ummai. Mulkinsa zai yaɗu daga teku zuwa teku, daga Kogi kuma zuwa ƙarshen duniya.
11 Also You—by the blood of Your covenant, I have sent Your prisoners out of the pit, There is no water in it.
Ke kuma, saboda jinin alkawarina da ke, zan’yantar da’yan kurkukunki daga rami marar ruwa.
12 Return to a stronghold, You prisoners of the hope, Even today a second announcer I restore to you.
Ku koma maɓuya, ya ku’yan kurkuku masu sa zuciya; ko yanzu ma na sanar cewa zan mayar muku ninki biyu.
13 For I have trodden for Myself with Judah, I have filled a bow [with] Ephraim, And I have stirred up your sons, O Zion, Against your sons, O Javan, And I have set you as the sword of a hero.”
Zan lanƙwasa Yahuda yadda nake lanƙwasa bakana, in kuma cika ta da Efraim kamar kibiya. Zan tā da’ya’yanki maza, ya Sihiyona, gāba da’ya’yanki, ya Girka, in kuma mai da ke kamar takobin jarumin yaƙi.
14 And YHWH appears for them, And His arrow has gone forth as lightning, And Lord YHWH blows with a horn, And He has gone with whirlwinds of the south.
Sa’an nan Ubangiji zai bayyana a bisansu; kibiyarsa za tă wulga kamar walƙiya. Ubangiji Mai Iko Duka zai busa ƙaho; zai taho ta cikin guguwa daga kudu,
15 YHWH of Hosts covers them over, And they consumed, and subdued sling-stones, Indeed, they have drunk, They have made a noise as wine, And they have been full as a bowl, As corners of an altar.
Ubangiji Maɗaukaki kuma zai tsare su. Za su hallakar su kuma yi nasara da duwatsun majajjawa. Za su sha su yi kururuwa kamar sun sha ruwan inabi; za su cika kamar kwanon da ake amfani don a yayyafa jini a kusurwoyin bagade.
16 And their God YHWH has saved them in that day, As a flock of His people, For stones of a crown are displaying themselves over His ground.
Ubangiji Allahnsu zai cece su a wannan rana gama su mutanensa ne da kuma garkensa. Za su haska a cikin ƙasarsa kamar lu’ulu’u a rawani.
17 For what His goodness! And what His beauty! Grain the young men, And new wine the virgins—make fruitful!
Za su yi kyan gani da kuma bansha’awa! Hatsi zai sa samari su yi murna, sabon ruwan inabi kuma zai sa’yan mata su yi farin ciki.