< Ruth 3 >

1 And her mother-in-law Naomi says to her, “My daughter, do I not seek rest for you, that it may be well with you?
Wata rana Na’omi surukar Rut ta ce mata, “’Yata, bai kamata in nema miki gida, inda za a tanada miki da kyau?
2 And now, is not Boaz of our acquaintance, with whose young women you have been? Behold, he is winnowing the threshing-floor of barley tonight,
Bowaz wanda kike aiki da bayinsa’yan mata ba danginmu ne na kusa ba? Da daren yau zai sussuka sha’ir nasa a masussuka.
3 and you have bathed, and anointed yourself, and put your garments on you, and gone down to the threshing-floor; do not let yourself be known to the man until he completes to eat and to drink;
Ki yi wanka ki fesa turare, ki kuma sa tufafinki mafi kyau. Sa’an nan ki gangara zuwa masussuka, amma kada ki bari yă san cewa kina a can sai ya gama ci da sha.
4 and it comes to pass, when he lies down, that you have known the place where he lies down, and have gone in, and uncovered his feet, and lain down—and he declares to you that which you do.”
Sa’ad da ya kwanta, ki lura da inda yake kwance. Sa’an nan ki tafi ki buɗe ƙafafunsa ki kwanta. Zai faɗa miki abin da za ki yi.”
5 And she says to her, “All that you say—I do.”
Rut ta amsa ta ce “Zan yi abin da kika faɗa.”
6 And she goes down [to] the threshing-floor, and does according to all that her mother-in-law commanded her
Saboda haka ta gangara zuwa masussuka ta kuma yi dukan abin da surukarta ta ce ta yi.
7 And Boaz eats and drinks, and his heart is glad; and he goes in to lie down at the end of the heap; and she comes in gently, and uncovers his feet, and lies down.
Sa’ad da Bowaz ya gama ci da sha yana kuma cikin farin ciki, sai ya tafi ya kwanta a ƙarshen tarin hatsi. Rut kuwa ta sulalle ta je ta buɗe ƙafafunsa ta kwanta.
8 And it comes to pass, at the middle of the night, that the man trembles, and turns himself, and behold, a woman is lying at his feet.
Da tsakar dare sai wani abu ya firgitar da mutumin, ya kuwa juya sai ya tarar da mace kwance a ƙafafunsa.
9 And he says, “Who [are] you?” And she says, “I [am] Ruth your handmaid, and you have spread your skirt over your handmaid, for you [are] a redeemer.”
Sai ya yi tambaya ya ce, “Ke wace ce?” Ta amsa ta ce, “Ni ce baranyarka Rut, ka rufe ni ta mayafinka da yake kai dangi, mai fansa ne na kusa.”
10 And he says, “Blessed [are] you of YHWH, my daughter; you have dealt more kindly at the latter end than at the beginning—not to go after the young men, either poor or rich.
Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji yă albarkace ki’yata. Wannan alheri ya fi wannan da kika nuna da farko. Ba ki gudu kin bi saurayi, mai arziki ko matalauci ba.
11 And now, my daughter, do not fear, all that you say I do to you, for all the gate of my people knows that you [are] a virtuous woman.
Yanzu kuwa’yata kada ki ji tsoro. Zan yi miki dukan abin da kika roƙa. Dukan’yan’uwana na gari sun san cewa ke mace ce mai halin kirki.
12 And now, surely, true, that I [am] a redeemer, but also there is a redeemer nearer than I.
Ko da yake gaskiya ne ni dangi ne na kusa, amma akwai dangi mai fansa mafi kusa fiye da ni.
13 Lodge tonight, and it has been in the morning, if he redeems you, well: he redeems; and if he does not delight to redeem you, then I have redeemed you—I; YHWH lives! Lie down until the morning.”
Ki kwana a nan, da safe kuwa in yana so yă fansa, to, da kyau, sai yă fansa. Amma in ba ya niyya, tabbatacce, na rantse da Ubangiji mai rai zan yi. Ki kwanta a nan sai da safe.”
14 And she lies down at his feet until the morning, and rises before one discerns another; and he says, “Let it not be known that the woman has come into the floor.”
Saboda haka ta kwanta a ƙafafunsa sai da safe, amma ta tashi kafin a gane wani, sai ya ce, “Kada ki bar wani yă san cewa mace ta zo masussuka.”
15 And he says, “Give the covering which [is] on you, and keep hold on it”; and she keeps hold on it, and he measures six [measures] of barley, and lays [it] on her; and he goes into the city.
Ya kuma ce, “Ki kawo gyalenki da kika yafa ki shimfiɗa shi a nan.” Sa’ad da ta yi haka, sai ya zuba mudu shida na sha’ir ya sa mata a kai. Sa’an nan ya koma gari.
16 And she comes to her mother-in-law, and she says, “Who [are] you, my daughter?” And she declares to her all that the man has done to her.
Sa’ad da Rut ta koma wurin surukarta Na’omi ta tambaye ta “Yaya aka yi’yata?” Sai ta faɗa mata dukan abin da Bowaz ya yi mata
17 And she says, “These six [measures] of barley he has given to me, for he said, You do not go in empty to your mother-in-law.”
ta kuma ƙara da cewa, “Ya ba ni waɗannan mudu shida na sha’ir, yana cewa, ‘Kada ki koma wurin surukarki hannu wofi.’”
18 And she says, “Sit still, my daughter, until you know how the matter falls, for the man does not rest except he has completed the matter today.”
Sai Na’omi ta ce, “Ki jira,’yata, sai kin ga abin da zai faru. Gama mutumin ba zai huta ba sai an warware batun a yau.”

< Ruth 3 >