< Romans 6 >

1 What, then, will we say? Will we continue in sin that grace may abound?
Me kuwa zamu ce yanzu? Sai mu ci gaba da yin zunubi domin Alheri ya yawaita?
2 Let it not be! We who died to sin—how will we still live in it?
Ba zai taba faruwa ba. 'Yaya za'ace mu da muka mutu cikin zunubi mu ci gaba da rayuwa cikin sa?
3 Are you ignorant that we, as many as were immersed into Christ Jesus, were immersed into His death?
Ba ku san cewa duk wadanda aka yi masu baftisma cikin Almasihu Yesu an yi masu baftisma har ya zuwa mutuwarsa ne ba?
4 We were buried together, then, with Him through the immersion into death, that even as Christ was raised up out of the dead through the glory of the Father, so we also might walk in newness of life.
An kuwa binne mu tare da shi, ta wurin baftisma cikin mutuwarsa. Haka kuma ya kasance ne domin kamar yadda Almasihu ya tashi daga matattu cikin daukakar Uba. Sakamakon haka muma zamu yi tafiya cikin sabuwar rayuwa.
5 For if we have become planted together to the likeness of His death, [so] we also will be of the resurrection;
Domin kuwa idan muna tare dashi cikin kamannin mutuwarsa zamu kuwa zauna tare dashi har ga kamannin tashinsa.
6 knowing this, that our old man was crucified with [Him], that the body of sin may be made useless, for our no longer serving sin,
Mun kuma san cewa, an giciye wannan tsohon mutunmin nan namu tare dashi, domin a hallaka jikin zunubi. wanna kuwa ya kasance ne domin kada mu ci gaba da bautar zunubi.
7 for he who has died has been set free from sin.
Duk kuma wanda ya mutu an ambace shi a matayin adali akan zunubi.
8 And if we died with Christ, we believe that we also will live with Him,
Amma idan muka mutu tare da Almasihu, mun bada gaskiya zamu yi rayuwa tare dashi.
9 knowing that Christ, having been raised up out of the dead, dies no more; death has no more lordship over Him;
Muna da sanen cewa an tada Almasihu daga matattu, don haka kuwa ba matacce yake ba. Mutuwa kuma bata da iko a kansa.
10 for in that He died, He died to sin once, and in that He lives, He lives to God;
Game da mutuwar da yayi ga zunubi yayi sau daya kuma domin dukka. Rayuwar da yake yi kuma yana yi wa Allah ne.
11 so also you, reckon yourselves to be dead indeed to sin, and living to God in Jesus Christ our Lord.
Don haka ku ma sai ku dauki kanku a matsayin matattu ga zunubi amma rayayyu ga Allah cikin Almasihu Yesu.
12 Do not let then sin reign in your mortal body, to obey it in its desires;
Sabili da haka kada ku bar zunubi yayi mulki a cikin jikinku, har ku yi biyayya ga sha'awarsa.
13 neither present your members instruments of unrighteousness to sin, but present yourselves to God as living out of the dead, and your members instruments of righteousness to God;
Kada ku mika gabobin jikinku ga zunubi a matsayin kayan aikin rashin adalci. Amma ku mika kanku ga Allah rayayyu daga mutuwa. Ku kuma mika gabobin jikinku ga Allah a matsayin kayan aiki na adalci.
14 for sin will not have lordship over you, for you are not under law, but under grace.
kada ku ba zunubi dama yayi mulki a kanku, domin ba karkashin doka kuke ba, amma karkashin alheri kuke.
15 What then? Will we sin because we are not under law but under grace? Let it not be!
To sai me? Sai mu yi zunubi wai don ba a karkashin doka muke ba amma alheri. ba zai taba faruwa ba.
16 Have you not known that to whom you present yourselves servants for obedience, servants you are to him to whom you obey, whether of sin to death, or of obedience to righteousness?
Ba ku san cewa duk ga wanda kuka mika kanku a matsayin bayi, a gareshi ku bayi ne ba? Wannan fa gaskiya ne, ko dai ku bayi ne ga zunubi wanda kaiwa ga mutuwa ko kuma bayi ga biyayya wanda ke kaiwa ga adalci.
17 And thanks to God, that you were servants of sin, and—were obedient from the heart to the form of teaching to which you were delivered up;
Amma godiya ta tabbata ga Allah! domin da ku bayin zunubi ne, amma kun yi biyayya daga zuciyarku irin salon koyarwar da aka baku.
18 and having been freed from sin, you became servants to righteousness.
An 'yantar daku daga bautar zunubi, an kuma maishe ku bayin adalci.
19 I speak in a human [way], because of the weakness of your flesh, for even as you presented your members servants to the uncleanness and to the lawlessness—to the lawlessness, so now present your members servants to righteousness—to sanctification,
Ina magana da ku kamar mutum, domin kasawarku ta nama da jini. Kamar yadda kuka mika gabobin jikinku ga kazamta da miyagun ayyuka, haka ma yanzu ku mika gabobin jikinku a matsayin bayi na adalci.
20 for when you were servants of sin, you were free from righteousness.
Domin a lokacin da kuke bayin zunubi, ku yantattu ne ga adalci.
21 What fruit, therefore, were you having then, in the things of which you are now ashamed? For the end of those [is] death.
A wannan lokacin wanne amfani kuka samu na ayyukan da yanzu kuke jin kunyarsu? Domin kuwa sakamakon wadannan ayyuka shine mutuwa.
22 And now, having been freed from sin, and having become servants to God, you have your fruit—to sanctification, and the end continuous life; (aiōnios g166)
Amma yanzu da da aka yantar daku daga zunubi aka mai da ku bayin Allah, amfaninsa ku kuwa shine tsarkakewarku. Sakamakon kuwa shine rai na har abada. (aiōnios g166)
23 for the wages of sin [is] death, and the gift of God [is] continuous life in Christ Jesus our Lord. (aiōnios g166)
Don kuwa sakamakon zunubi mutuwa ne. Amma kyautar Allah itace rai madauwami cikin Almasihu Yesu Ubangijinmu. (aiōnios g166)

< Romans 6 >