< Romans 4 >

1 What, then, will we say Abraham our father to have found, according to flesh?
Me kenan zamu ce game da Ibrahim, kakanmu a jiki, me ya samu?
2 For if Abraham was declared righteous by works, he has to boast—but not before God;
Domin idan Ibrahim ya sami kubutarwa ta wurin ayuka, ai da ya sami dalilin fahariya, amma ba a gaban Allah ba.
3 for what does the writing say? “And Abraham believed God, and it was reckoned to him for righteousness”;
Kuma fa me nassi ke fadi? “Ibrahim ya bada gaskiya ga Allah, sai aka lisafta ta adalci gare shi.”
4 and to him who is working, the reward is not reckoned of grace, but of debt;
Yanzu fa shi dake yin ayyuka, ladansa ba a lisafta shi alheri ba ne, amma abun da ke nasa.
5 and to him who is not working, and is believing on Him who is declaring righteous the impious, his faith is reckoned for righteousness—
Amma kuma shi da bai da ayyuka kuma maimakon haka ya gaskanta ga wanda ke kubutar da masu zunubai, bangaskiyarsa an lisafta ta a misalin adalci.
6 even as David also speaks of the blessedness of the man to whom God reckons righteousness apart from works:
Dauda ya yi furcin albarka bisa mutumin da Allah ya lisafta mai adalci da rashin ayyuka.
7 “Blessed [are] they whose lawless acts were forgiven, And whose sins were covered;
Sai ya ce, “Masu albarka ne wadanda aka yafe laifofinsu, kuma wadanda zunubansu a rufe suke.
8 Blessed [is] the man To whom the LORD may not reckon sin.”
Mai albarka ne mutumin da ko kadan Ubangiji ba zaya lisafta zunubin sa ba.”
9 [Is] this blessedness, then, on the circumcision, or also on the uncircumcision—for we say that faith was reckoned to Abraham for righteousness?
To albarkar da aka fadi ko a bisansu wadanda aka yi wa kaciya ne kadai, ko kuwa a bisan su ma marasa kaciya? Domin mun yi furcin, “Bangaskiyar Ibrahim an lisafta ta adalci ce agare shi.”
10 How then was it reckoned? He being in circumcision, or in uncircumcision? Not in circumcision, but in uncircumcision;
Yaya aka lisafta ta? Bayan Ibrahim ya yi kaciya, ko kuwa a rashin kaciya? Ba a cikin kaciya ba, amma a rashin kaciya.
11 and he received a sign of circumcision, a seal of the righteousness of faith in the uncircumcision, for his being father of all those believing through uncircumcision, for the righteousness also being reckoned to them,
Ibrahim ya amshi alamar kaciya. Wannan shi ne hatimin adalcin bangaskiyar da ya ke da ita tun cikin rashin kaciyarsa. Albarkacin wannan alama ce, ta sa shi ya zama uban dukkan wadanda suka badagaskiya, ko da shike ba su da kaciya. Wato ma'ana, adalci za a lisafta masu.
12 and father of circumcision to those not of circumcision only, but who also walk in the steps of faith, that [is] in the uncircumcision of our father Abraham.
Wannan kuma yana da ma'anar cewa Ibrahim ya zama uban kaciya ga wadanda suka fito ba domin masu kaciya kadai ba, amma kuma domin wadanda ke biyo matakin ubanmu Ibrahim. Kuma wannan itace bangaskiyar da ya ke da ita a rashin kaciya.
13 For not through law [is] the promise to Abraham, or to his seed, of his being heir of the world, but through the righteousness of faith;
Domin ba ta wurin shari'a aka bada alkawarin nan da aka yi wa Ibrahim da zuriyarsa ba, wannan alkawarin da ya ce zasu gaji duniya. Maimako, a ta wurin adalcin bangaskiya ne.
14 for if they who are of law [are] heirs, faith has been made void, and the promise has been made useless;
Domin idan su da ke na shari'a magada ne, bangaskiya bata da komai, kuma alkawarin an wofintar da shi kenan.
15 for the Law works wrath; for where law is not, neither [is] transgression.
Domin shari'a ta kan jawo fushi, amma ta wurin rashin shari'a, babu karya umarni.
16 Because of this [it is] of faith, that [it may be] according to grace, for the promise being sure to all the seed, not to that which [is] of the Law only, but also to that which [is] of the faith of Abraham,
Saboda wannan dalili haka ta faru ta wurin bangaskiya, domin ya zama bisa ga alheri. Kamar haka, alkawarin ya tabbata ga dukkan zuriya. Kuma wannan zuriya ba zata kunshi wadanda suke da sanin shari'a ba kadai, har ma da wadanda ke daga bangaskiyar Ibrahim. Saboda shi ne uban dukkan kowa,
17 who is father of us all (according as it has been written: “A father of many nations I have set you,”) before Him whom he believed—God, who is quickening the dead, and is calling the things that are not as being.
kamar yadda aka rubuta, “Na maishe ka uba ga kasashe masu yawa.” Ibrahim na gaban aminin sa, wato, Allah, mai bada rai ga mattatu kuma ya kan kira abubuwan da basu da rai su kuma kasance.
18 Who, against hope, believed in hope, for his becoming father of many nations according to that spoken: “So will your seed be”;
Duk da halin da ke a bayyane, Ibrahim ya gaskata ga Allah kai tsaye game da abubuwan da ke nan gaba. Sai ya zama uba ga kasashe masu yawa, kamar yadda aka ambata, “... Haka zuriyarka zata kasance.”
19 and having not been weak in faith, he did not consider his own body, already become dead (being about one hundred years old), and the deadness of Sarah’s womb,
Ba ya karaya a bangaskiya ba. Ibrahim ya yarda da cewa jikinsa ya rigaya ya tsufa (shekarun sa na misalin dari). Ya kuma yarda da cewa mahaifar Saratu bata iya bada 'ya'ya ba.
20 and at the promise of God did not stagger in unbelief, but was strengthened in faith, having given glory to God,
Amma domin alkawarin Allah, Ibrahim bai ji nauyin rashin bangaskiya ba. Maimakon haka, ya sami karfafawa a bangaskiyarsa sai ya daukaka Allah.
21 and having been fully persuaded that what He has promised He is also able to do:
Ya na da cikakkiyar gamsuwa cewa idan Allah ya yi alkawari, shi mai iya kammalawa ne.
22 for this reason also it was reckoned to him for righteousness.
Haka nan ne kuma aka lisafta masa wannan a matsayin adalci.
23 And it was not written on his account alone that it was reckoned to him,
To ba'a rubuta kawai damin amfaninsa kadai ba, da aka lisafta dominsa.
24 but also on ours, to whom it is about to be reckoned—to us believing on Him who raised up Jesus our Lord out of the dead,
A rubuce yake domin mu, domin wadanda za'a lisafta su, mu da muka bada gaskiya gare shi wanda ya tada Yesu Ubangijinmu daga matattu.
25 who was delivered up because of our offenses, and was raised up because of our being declared righteous.
Wannan shi ne wanda aka bashe shi domin zunubanmu kuma an tada shi saboda fasar mu.

< Romans 4 >