< Romans 10 >
1 Brothers, the pleasure indeed of my heart, and my supplication that [is] to God for Israel, is—for salvation;
’Yan’uwa, abin da zuciyata take so da kuma addu’ata ga Allah saboda Isra’ilawa shi ne su sami ceto.
2 for I bear them testimony that they have a zeal of God, but not according to knowledge,
Gama na shaida su a kan suna da kishi bin Allah, sai dai kishinsu ba a bisa sani ba.
3 for not knowing the righteousness of God, and seeking to establish their own righteousness, they did not submit to the righteousness of God.
Da yake ba su san adalcin da yake fitowa daga Allah ba suka kuma nemi su kafa nasu, sai suka ƙi miƙa kai ga adalcin Allah.
4 For Christ is an end of law for righteousness to everyone who is believing,
Kiristi shi ne ƙarshen doka domin a sami adalci wa kowane mai bangaskiya.
5 for Moses describes the righteousness that [is] of the Law, that, “The man who did them will live in them,”
Musa ya bayyana adalcin da yake ga Doka cewa, “Mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu.”
6 and the righteousness of faith thus speaks: “You may not say in your heart, Who will go up to Heaven?” (that is, to bring Christ down)
Amma adalcin da yake ga bangaskiya yana cewa, “Kada ka faɗa a zuciyarka, ‘Wa zai hau sama?’” (wato, don yă sauko da Kiristi),
7 or, “Who will go down to the abyss?” (that is, to bring up Christ out of the dead). (Abyssos )
“ko kuwa ‘Wa zai gangara can zurfin ƙasa?’” (wato, don yă hauro da Kiristi daga matattu). (Abyssos )
8 But what does it say? “The saying is near you—in your mouth, and in your heart”: that is, the saying of the faith that we preach;
Amma mene ne aka ce? “Maganar tana kusa da kai; tana cikin bakinka da kuma cikin zuciyarka,” wato, maganar bangaskiyan nan da muke shela.
9 that if you may confess with your mouth that Jesus [is] LORD, and may believe in your heart that God raised Him out of the dead, you will be saved,
Cewa in ka furta da bakinka, “Yesu Ubangiji ne,” ka kuma gaskata a zuciyarka cewa Allah ya tā da shi daga matattu, za ka sami ceto.
10 for with the heart [one] believes to righteousness, and with the mouth is confession made to salvation;
Gama da zuciyarka ce kakan gaskata a kuma kuɓutar da kai, da bakinka ne kuma kake furta a kuma cece ka.
11 for the Writing says, “Everyone who is believing on Him will not be ashamed,”
Kamar yadda Nassi ya ce, “Duk wanda ya gaskata da shi ba zai taɓa shan kunya ba.”
12 for there is no difference between Jew and Greek, for the same Lord of all [is] rich to all those calling on Him,
Gama ba bambanci tsakanin mutumin Yahuda da mutumin Al’ummai, Ubangijin nan ɗaya shi ne Ubangijin kowa yana kuma ba da albarka a yalwace ga duk masu kira gare shi,
13 for “Everyone who, if he may have called on the Name of the LORD, will be saved.”
gama, “Duk wanda ya kira bisa sunan Ubangiji zai sami ceto.”
14 How then will they call on [Him] in whom they did not believe? And how will they believe [on Him] of whom they did not hear? And how will they hear apart from one preaching?
To, ta yaya za su kira ga wanda ba su gaskata ba? Ta yaya kuma za su gaskata wanda ba su taɓa ji ba? Ta yaya kuma za su ji ba tare da wani ya yi musu wa’azi ba?
15 And how will they preach, if they may not be sent? According as it has been written: “How beautiful the feet of those proclaiming good tidings of peace, of those proclaiming good tidings of the good things!”
Kuma ta yaya za su yi wa’azi in ba an aike su ba? Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Isowar masu kawo labari mai daɗi abu mai kyau ne ƙwarai!”
16 But they were not all obedient to the good tidings, for Isaiah says, “LORD, who gave credence to our report?”
Amma ba dukan Isra’ilawa ne suka karɓi labari mai daɗin nan ba. Gama Ishaya ya ce, “Ubangiji, wa ya gaskata saƙonmu?”
17 So then faith [is] by a report, and the report through a saying of God,
Saboda haka, bangaskiya takan zo ne ta wurin jin saƙo, akan ji saƙon kuma ta wurin maganar Kiristi.
18 but I say, did they not hear? Yes, indeed, “their voice went forth to all the earth, and their sayings to the ends of the habitable world.”
Amma ina tambaya, “Ba su ji ba ne? Tabbatacce sun ji. “Muryarsu ta tafi ko’ina a cikin duniya, kalmominsu kuma har iyakar duniya.”
19 But I say, did Israel not know? First Moses says, “I will provoke you to jealousy by [that which is] not a nation, By an unintelligent nation I will anger you,”
Har wa yau, ina da tambaya. Shin, Isra’ila ba su fahimta ba ne? Da farko, Musa ya ce, “Zan sa ku yi kishin waɗanda ba al’umma ba; zan sa ku yi fushin al’ummar da ba ta da fahimta.”
20 and Isaiah is very bold and says, “I was found by those not seeking Me; I became visible to those not inquiring after Me”;
Ishaya kuma ya fito gabagadi ya ce, “Waɗanda ba su neme ni ba, su suka same ni; Na bayyana kaina ga waɗanda ba su ma taɓa neman sanina ba.”
21 and to Israel He says, “All the day I stretched out My hands to a people unbelieving and contradicting.”
Amma game da Isra’ila ya ce, “Dukan yini na miƙa hannuwana ga mutane marasa biyayya da masu taurinkai.”