< Revelation 7 >

1 And after these things I saw four messengers, standing on the four corners of the earth, holding the four winds of the earth, that the wind may not blow on the earth, nor on the sea, nor on any tree;
Bayan wannan sai na ga mala'iku hudu suna tsaye bisa kusurwoyi hudu na duniya, suka rike iskoki hudu na duniya kamkam domin kada iska ta hura a kan duniya, a kan teku, ko wani itace.
2 and I saw another messenger going up from the rising of the sun, having a seal of the living God, and he cried with a great voice to the four messengers, to whom it was given to injure the land and the sea, saying,
Sai na ga wani mala'ika na zuwa daga gabas, wanda yake da hatimin Allah mai rai. Ya yi kira da babbar murya da mala'ikun nan hudu da aka basu dama su azabtar da duniya da teku:
3 “Do not injure the land, nor the sea, nor the trees, until we may seal the servants of our God on their foreheads.”
“Kada ku azabtar da duniya, da teku, da itatuwa har sai mun sa hatimi bisa goshin bayin Allahnmu.”
4 And I heard the number of those sealed—one hundred forty-four thousand, having been sealed out of every tribe of the sons of Israel:
Sai naji yawan wadanda aka hatimce: 144, 000, wadanda aka hatimce daga kowacce kabilar mutanen Isra'ila:
5 of the tribe of Judah twelve thousand were sealed; of the tribe of Reuben twelve thousand were sealed; of the tribe of Gad twelve thousand were sealed;
dubu goma sha biyu aka hatimce daga kabilar Yahuza, dubu goma sha biyu daga kabilar Ra'ubainu, dubu goma sha biyu daga kabilar Gad,
6 of the tribe of Asher twelve thousand were sealed; of the tribe of Naphtali twelve thousand were sealed; of the tribe of Manasseh twelve thousand were sealed;
dubu goma sha biyu daga kabilar Ashiru, dubu goma sha biyu daga kabilar Naftali, dubu goma sha biyu daga kabilar Manassa.
7 of the tribe of Simeon twelve thousand were sealed; of the tribe of Levi twelve thousand were sealed; of the tribe of Issachar twelve thousand were sealed;
Dubu goma sha biyu daga kabilar Saminu, dubu goma sha biyu daga kabilar Lawi, dubu goma sha biyu daga kabilar Issaka,
8 of the tribe of Zebulun twelve thousand were sealed; of the tribe of Joseph twelve thousand were sealed; of the tribe of Benjamin twelve thousand were sealed.
dubu goma sha biyu daga kabilar zabaluna, dubu goma sha biyu daga kabilar Yusufu, sai kuma dubu goma sha biyu daga kabilar Bilyaminu aka hatimce.
9 After these things I saw, and behold, a great multitude, which no one was able to number, out of all nations, and tribes, and peoples, and tongues, standing before the throne, and before the Lamb, having been clothed [in] white robes, and palms in their hands,
Bayan wadannan abubuwa na duba, sai ga wani babban taro wanda ba mai iya kirgawa daga kowacce al'umma, kabila, mutane da harsuna tsaye a gaban kursiyin da gaban Dan Ragon. Suna sanye da fararen tufafi da ganyen dabino a hannuwansu,
10 and crying with a great voice, saying, “Salvation to our God, the [One] sitting on the throne, and to the Lamb!”
kuma suna kira da murya mai karfi: “Ceto ya tabbata ga Allahnmu wanda ke zaune bisa kursiyi, da kuma Dan Ragon!”
11 And all the messengers stood around the throne, and the elders and the four living creatures, and they fell on their faces and worshiped God,
Dukan mala'iku suna tsaitsaye kewaye da kursiyin kuma kewaye da dattawan nan da kuma rayayyun halittun nan hudu, suka kwanta rib da ciki da fuskokinsu a gaban kursiyin. Suka yi sujada ga Allah,
12 saying, “Amen! The blessing, and the glory, and the wisdom, and the thanksgiving, and the honor, and the power, and the strength, [are] to our God through the ages of the ages! Amen!” (aiōn g165)
suna cewa, “Amin! yabo, daukaka, hikima, godiya, girma, iko, da karfi su zama na Allahnmu har abada abadin! Amin!” (aiōn g165)
13 And one of the elders answered, saying to me, “These having been clothed with the white robes, who are they, and from where have they come?”
Sai daya daga cikin dattawan ya tambaye ni, “Su wanene wadannan, da suke sanye da fararen tufafi, kuma daga ina suka fito?”
14 And I have said to him, “Lord, you have known”; and he said to me, “These are those who are coming out of the Great Tribulation, and they washed their robes, and they made their robes white in the blood of the Lamb;
Sai nace masa, “Ya shugaba, “Ka sani,” sai ya ce mani, “Wadannan sune suka fito daga babban tsanani. Sun wanke tufafin su sun maida su farare cikin jinin Dan Ragon.
15 because of this they are before the throne of God, and they do service to Him day and night in His temple, and He who is sitting on the throne will dwell over them;
Domin wannan dalili, suke gaban kursiyin Allah, kuma suna masa sujada dare da rana cikin haikalinsa. Shi wanda ke zaune bisa kursiyin zai zama runfa a bisan su.
16 they will not hunger anymore, nor may the sun fall on them, nor any heat,
Ba za su kara jin yunwa ba, ko kishin ruwa ba. Rana ba zata buge su ba, ko kowanne zafi mai kuna.
17 because the Lamb that [is] in the midst of the throne will feed them, and will lead them to living fountains of waters, and God will wipe away every tear from their eyes.”
Domin Dan Ragon dake tsakiyar kursiyin zai zama makiyayin su, kuma zai bishe su zuwa mabulbulan ruwan rai, kuma Allah zai share dukan hawaye daga idanuwansu.”

< Revelation 7 >