< Revelation 16 >
1 And I heard a great voice out of the temple saying to the seven messengers, “Go away, and pour out the bowls of the wrath of God into the earth”;
Na ji babban murya na kira daga cikin haikali tana ce wa malai'iku bakwai, ''Ku je ku zuba tasoshi bakwai na fushin Allah a kan duniya.”
2 and the first went away, and poured out his bowl into the earth, and there came a sore—bad and grievous—to men, those having the mark of the beast, and those worshiping his image.
Mala'ika na fari ya je ya zuba tasarsa a kan duniya; munanan gyambuna masu zafi suka fito wa mutane wadanda suke da alamar dabbar, wadanda suka bauta wa siffarsa.
3 And the second messenger poured out his bowl into the sea, and it became blood as of [one] dead, and every living soul in the sea died.
Mala'ika na biyu ya zuba tasarsa cikin teku. Ya zama jini, kamar jinin wanda ya mutu, kuma kowane abu mai rai da ke cikin tekun ya mutu.'
4 And the third messenger poured out his bowl into the rivers, and into the fountains of the waters, and there came blood,
Malaika na uku ya zuba tasarsa a cikin rafuffuka da mabulbulan ruwa, sai suka zama jini.
5 and I heard the messenger of the waters, saying, “Righteous, O LORD, are You, who is, and who was, [[and who will be, ]] the Holy [One], because You judged these things,
Na ji mala'ikan ruwaye ya ce, ''Kai mai adalci ne - wanda ya ke yanzu wanda yake kuma a da, Mai Tsarkin nan, domin ka shari'anta wadannan abubuwa.
6 because they poured out [the] blood of holy ones and prophets, and You gave to them blood to drink, for they are worthy”;
Domin sun zubar da jinin masu ba da gaskiya da annabawa, ka basu jini su sha; shine abinda da ya dace da su.
7 and I heard another out of the altar, saying, “Yes, LORD God, the Almighty, true and righteous [are] Your judgments.”
Na ji bagadi ya amsa, ''I, Ubangiji Allah Mai iko duka, shari'un ka gaskiya ne da adalci.''
8 And the fourth messenger poured out his bowl on the sun, and there was given to him to scorch men with fire,
Mala'ika na hudu ya zuba tasarsa a kan rana, kuma aka ba shi izini ya kone jama'a da wuta.
9 and men were scorched with great heat, and they slandered the Name of God, who has authority over these plagues, and they did not convert—to give to Him glory.
Suka kone da zafi mai tsanani, kuma suka sabi sunan Allah, wanda ke da iko akan annobai. Ba su tuba ba ko su daukaka shi.
10 And the fifth messenger poured out his bowl on the throne of the beast, and his kingdom became darkened, and they were gnawing their tongues from the pain,
Sai malaika na biyar ya zuba tasarsa a kan kursiyin dabban, sai duhu ya rufe mulkinsa. Suka cicciji harsunansu saboda zafi.
11 and they slandered the God of Heaven, from their pains, and from their sores, and they did not convert from their works.
Suka yi sabon Allah na sama domin zafi da gyambunansu, suka kuma ki su tuba daga abin da suka yi.
12 And the sixth messenger poured out his bowl on the great river, the Euphrates, and its water was dried up, that the way of the kings who are from the rising of the sun may be made ready;
Mala'ika na shida ya zuba tasarsa cikin babban rafi, Yufiretis. Ruwansa ya bushe domin a shirya hanya da sarakuna za su zo daga gabas.
13 and I saw [come] out of the mouth of the dragon, and out of the mouth of the beast, and out of the mouth of the false prophet, three unclean spirits like frogs—
Na ga kazamun ruhohi uku suna kama da kwadin da ke fitowa daga bakin diragon, da makaryacin annabi.
14 for they are spirits of demons, doing signs—which go forth to the kings of the earth, and of the whole world, to bring them together to the battle of that great day of God the Almighty.
Gama su ruhohin aljanu ne masu aikata alamun ban mamaki. Sun fita za su wurin sarakunan dukan duniya domin su tattaro su wuri daya saboda yaki a babbar ranar Allah Mai iko duka.
15 (“Behold, I come as a thief; blessed [is] he who is watching, and keeping his garments, that he may not walk naked, and they may see his unseemliness.”)
(''Duba! Ina zuwa kamar barawo! Mai albarka ne wanda ke zaune a fadake, wanda ke sanye da tufafinsa domin ba zai fita tsirara a ga tsiraicin sa ba.”)
16 And they brought them together to the place that is called in Hebrew Armageddon.
Aka kawo su tare a wurin da ake kira Armagiddon da Ibraniyanci.
17 And the seventh messenger poured out his bowl on the air, and there came forth a great voice from the temple of Heaven, from the throne, saying, “It is done!”
Mala'ika na bakwai ya zuba tasarsa cikin iska. Sa'annan babbar murya ta fito daga cikin haikali da kuma kursiyin, cewa, ''An gama!''
18 And there came voices, and thunders, and lightnings; and a great earthquake came, such as has not come since men came on the earth, so mighty an earthquake—so great!
Aka yi walkiya, da kararraki masu tsanani, da aradu da babbar girgizar kasa - girgizar da ta fi kowacce da aka taba yi tun da 'yan adam suke a duniya, girgizar da girma ta ke.
19 And it came—the great city—into three parts, and the cities of the nations fell, and Babylon the great was remembered before God, to give to her the cup of the wine of the wrath of His anger,
Babban birnin ya rabu kashi uku, kuma biranen al'ummai suka fadi. Sai Allah ya tuna da Babila mai girma, sai ya ba wancan birnin koko cike da ruwan innabi wanda aka yi daga fushinsa mai tsanani.
20 and every island fled away, and mountains were not found,
Kowanne tsibiri ya bace, sai ba a kara ganin duwatsun ba.
21 and great hail (as of talent weight) comes down out of the sky on men, and men slandered God because of the plague of the hail, because its plague is very great.
Manyan duwatsun kankara, masu nauyin talanti, suka fado daga sama kan mutane. Suka zagi Allah domin annobar kankarar saboda annobar ta yi tsanani.