< Revelation 12 >
1 And a great sign was seen in the sky: a woman clothed with the sun, and the moon under her feet, and on her head a garland of twelve stars,
Babbar alama mai banmamaki ta bayyana a sama, mace tana lulluɓe da rana, da kuma wata a ƙarƙashin sawunta, akwai kuma rawani mai taurari goma sha biyu a kanta.
2 and having [a child] in [her] womb she cries out, travailing and being in pain to bring forth.
Tana da ciki ta kuma yi kuka mai zafi yayinda take gab da haihuwa.
3 And there was seen another sign in the sky, and behold, a great fire-colored dragon, having seven heads and ten horns, and seven crowns on his heads,
Sai wata alama ta bayyana a sama, wani babban jan maciji mai kawuna bakwai da ƙahoni goma da rawani bakwai a kan kawunansa.
4 and his tail draws the third of the stars of the sky, and he cast them to the earth; and the dragon stood before the woman who is about to bring forth, that when she may bring forth, he may devour her child;
Wutsiyarsa ta share kashi ɗaya bisa uku na taurari daga sararin sama ta kuma zubar da su ƙasa. Ƙaton jan macijin ya tsaya a gaban macen wadda take gab da haihuwa, don yă cinye ɗanta nan take bayan an haife shi.
5 and she brought forth a male son, who is about to rule all the nations with a rod of iron, and her child was snatched up to God and to His throne,
Ta haifi ɗa, namiji, wanda zai yi mulkin dukan al’ummai da sandar ƙarfe. Aka fyauce ɗanta zuwa wurin Allah da kuma kursiyinsa.
6 and the woman fled into the wilderness, where she has a place made ready from God, that there they may nourish her—one thousand, two hundred, sixty days.
Sai macen ta gudu zuwa hamada zuwa inda Allah ya shirya dominta, inda za a lura da ita har kwana 1,260.
7 And there came war in Heaven: Michael and his messengers warred against the dragon, and the dragon and his messengers warred,
Aka kuwa yi yaƙi a sama. Mika’ilu da mala’ikunsa yaƙi macijin, maciji da mala’ikunsa su ma suka mai da martani.
8 and they did not prevail, nor was their place found anymore in Heaven;
Amma macijin nan ba shi da isashen ƙarfi, har suka rasa matsayinsu a sama.
9 and the great dragon was cast forth—the old serpent, who is called “Devil,” and “Satan,” who is leading the whole world astray—he was cast forth to the earth, and his messengers were cast forth with him.
Aka jefar da ƙaton jan macijin ƙasa, tsohon maciji nan da ake kira Iblis, ko Shaiɗan, wanda ya ɓad da dukan duniya. Aka jefar da shi ƙasa, tare da mala’ikunsa a duniya.
10 And I heard a great voice saying in Heaven, “Now came the salvation, and the power, and the kingdom, of our God, and the authority of His Christ, because the accuser of our brothers was cast down, who is accusing them before our God day and night;
Sa’an nan na ji babbar murya daga sama tana cewa, “Yanzu ceto da iko da mulkin Allahnmu, da kuma ikon Kiristinsa. Gama mai zargin’yan’uwanmu, wanda yake zarginsu a gaban Allahnmu dare da rana, an jefar da shi ƙasa.
11 and they overcame him because of the blood of the Lamb, and because of the word of their testimony, and they did not love their life—to death;
Sun ci nasara a kansa ta wurin jinin Ɗan Ragon da ta wurin kalmar shaidarsu; ba su ƙaunaci rayukansu sosai har da za su ja da baya daga mutuwa.
12 because of this be glad, you heavens, and those who dwell in them; woe to those inhabiting the earth and the sea, because the Devil went down to you, having great wrath, having known that he has [a] short time.”
Saboda haka ku yi farin ciki, ku sammai, da ku da kuke zaune a cikinsu! Amma kaiton duniya da kuma teku, gama Iblis ya sauko gare ku! Ya cika da fushi, domin ya san cewa lokacinsa ya rage kaɗan.”
13 And when the dragon saw that he was cast forth to the earth, he pursued the woman who brought forth the male,
Sa’ad da macijin ya ga an jefar da shi a duniya, sai ya fafari macen nan da ta haifi ɗa namiji.
14 and there were given to the woman two wings of the great eagle, that she may fly into the wilderness, to her place, where she is nourished a time, and times, and half a time, from the face of the serpent;
Sai aka ba wa macen fikafikai biyu na babban gaggafa, don ta tashi sama zuwa inda aka shirya mata a hamada, inda za a lura da ita na ɗan lokaci, lokuta da rabin lokaci, inda macijin ba zai iya kaiwa ba.
15 and the serpent cast forth out of his mouth water as a river after the woman, that he may cause her to be carried away by the river,
Sa’an nan daga bakinsa macijin ya kwarara ruwa kamar kogi, don ruwan ya cimma matan yă kuma kwashe ta tare da ambaliya.
16 and the earth helped the woman, and the earth opened its mouth and swallowed up the river that the dragon cast forth out of his mouth;
Amma ƙasa ta taimaki macen ta wurin buɗe bakinta ta kuma shanye ruwan kogin da macijin ya kwarara daga bakinsa.
17 and the dragon was angry against the woman, and went away to make war with the rest of her seed, those keeping the commands of God, and having the testimony of Jesus.
Sai macijin ya yi fushi da macen ya kuma koma wajen sauran zuriyarta don yă yaƙe su waɗannan waɗanda suke biyayya da umarnan Allah suke kuma riƙe da shaidar Yesu.