< Revelation 11 >

1 And there was given to me a reed like to a rod, [[and the messenger stood, ]] saying, “Rise, and measure the temple of God, and the altar, and those worshiping in it;
Aka bani sanda in yi amfani da ita kamar sandar awo. Aka ce mani, “Tashi ka auna haikalin Allah da bagadi, da wadanda ke sujada a cikinsa.
2 and leave out the court that is outside the temple, and you may not measure it, because it was given to the nations, and they will tread down the holy city forty-two months;
Amma kada ka auna harabar haikalin, domin an ba da shi ga Al'ummai. Za su tattake birnin mai tsarki har wata arba'in da biyu.
3 and I will give to My two witnesses, and they will prophesy one thousand, two hundred, sixty days, clothed with sackcloth”;
Zan ba shaidu na biyu iko su yi anabci na kwanaki dubu daya da dari biyu da sittin, sanye da tsummoki.
4 these are the two olive [trees], and the two lampstands that stand before the God of the earth;
Wadannan shaidu sune itatuwan zaitun biyu da kuma fitilu biyu da suke tsaye a gaban Ubangijin duniya.
5 and if anyone may will to injure them, fire proceeds out of their mouth, and devours their enemies, and if anyone may will to injure them, thus it is required of him to be killed.
Idan wani ya yi niyyar cutar da su, wuta na fitowa daga bakinsu ta lashe makiyansu. Duk mai son cutar da su, dole a kashe shi ta wannan hanya.
6 These have authority to shut the sky, that rain may not rain in the days of their prophecy, and they have authority over the waters to turn them to blood, and to strike the land with every plague, as often as they may will.
Wadannan shaidu suna da iko su kulle sama domin kada a yi ruwa a lokacin da suke anabci. Suna da iko su juya ruwaye su zama jini, su kuma bugi duniya da kowacce irin annoba duk lokacin da suka ga dama.
7 And when they may finish their testimony, the beast that is coming up out of the abyss will make war with them, and overcome them, and kill them, (Abyssos g12)
Sa'adda suka gama shaidarsu, dabban da ke fitowa daga rami marar iyaka zai yi yaki da su. Zai ci nasara da su ya kashe su. (Abyssos g12)
8 and their body [is] on the street of the great city that is called spiritually Sodom and Egypt, where also their Lord was crucified,
Gawawwakinsu zasu kwanta kan hanyar babban birnin nan (wanda ma'anar sa ake kira Saduma da Masar) inda aka gicciye Ubangijinsu.
9 and they gaze—[those] of the peoples, and tribes, and tongues, and nations—on their dead bodies three and a half days, and they will not allow their dead bodies to be put into tombs,
Wajen kwana uku da rabi wadansu daga dukan mutane, da kabila, da harshe, da al'umma za su yi kallon gawawwakinsu. Za su ki yarda a sa su cikin kabari.
10 and those dwelling on the earth will rejoice over them, and will make merry, and they will send gifts to one another, because these—the two prophets—tormented those dwelling on the earth.
Mazaunan duniya zasu yi murna da biki a kansu. Har za su aika wa juna kyautai saboda annabawan nan biyu da suka azabtar da mazaunan duniya.
11 And after the three and a half days, [the] Spirit of life from God entered into them, and they stood on their feet, and great fear fell on those beholding them,
Amma bayan kwana uku da rabi, numfanshin rai daga wurin Allah zai shiga cikinsu sa'annan za su tsaya a kan kafafunsu. Matsanancin tsoro zata fado kan wadanda za su gansu.
12 and they heard a great voice out of Heaven saying to them, “Come up here”; and they went up to Heaven in the cloud, and their enemies beheld them;
Sa'annan zasu ji murya mai kara daga sama tana ce masu, “Ku hauro nan!” Sa'annan za su tafi sama cikin gajimarai, makiyansu suna kallo.
13 and in that hour a great earthquake came, and the tenth of the city fell, and seven thousand names of men were killed in the earthquake, and the rest became frightened, and they gave glory to the God of Heaven.
A waccan sa'a za a yi babbar girgizar kasa, sai kashi daya cikin goma na garin ya fadi. Mutane dubu bakwai za su mutu a girgizar kasar, wadanda suka tsira kuwa za su tsorata su ba da daukaka ga Allah na sama.
14 The second woe went forth, behold, the third woe comes quickly.
Annoba ta biyu ta wuce. Duba! Annoba ta uku tana zuwa nan da nan.
15 And the seventh messenger sounded the trumpet, and there came great voices in Heaven, saying, “The kingdoms of the world became [those] of our Lord and of His Christ, and He will reign through the ages of the ages!” (aiōn g165)
Sa'annan mala'ika na bakwai ya busa kahonsa, sai muryoyi masu kara suka yi magana cikin sama cewa, “Mulkin duniya ya zama mulkin Ubangijinmu da na Almasihunsa. Zai yi mulki har abada abadin.” (aiōn g165)
16 And the twenty-four elders, who are sitting on their thrones before God, fell on their faces and worshiped God,
Sa'annan dattawan nan ashirin da hudu da ke zaune a kursiyoyinsu a gaban Allah, suka fadi fuskokinsu na kasa. Suka yi wa Allah sujada.
17 saying, “We give thanks to You, O LORD God, the Almighty, who is, and who was, and who is coming, because You have taken Your great power and reigned;
Suka ce, “Mun yi maka godiya, Ubangiji Allah, Madaukaki, wanda yake yanzu da wanda yake a da, saboda ka dauki ikonka mai girma ka fara mulki.
18 and the nations were angry, and Your anger came, and the time of the dead to be judged, and to give the reward to Your servants, to the prophets, and to the holy ones, and to those fearing Your Name, to the small and to the great, and to destroy those who are destroying the earth.”
Al'ummai suka fusata, amma hasalar ka ta zo. Lokaci ya zo da za a yi wa mattatu sharia, da zaka ba da sakamako ga bayinka annabawa, da masu ba da gaskiya, da wadanda suka ji tsoron sunanka, karami da babba. Lokaci kuma ya yi da za ka hallaka wadanda ke hallakar da duniya.”
19 And the temple of God was opened in Heaven, and the Ark of His Covenant was seen in His temple, and there came lightnings, and voices, and thunders, and an earthquake, and great hail.
Sa'annan aka bude haikalin Allah da ke sama, sai aka ga akwatin alkawarinsa a cikin haikalinsa. Sai ga hasken walkiya, da rugugi, da aradu, da girgizar kasa, da manyan duwatsun kankara.

< Revelation 11 >