< Psalms 95 >

1 Come, we sing to YHWH, We shout to the rock of our salvation.
Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
2 We come before His face with thanksgiving, We shout to Him with psalms.
Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
3 For YHWH [is] a great God, And a great King over all gods.
Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
4 In whose hand [are] the deep places of earth, And the strong places of hills [are] His.
A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
5 Whose is the sea, and He made it, And His hands formed the dry land.
Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
6 Come in, we bow ourselves, and we bend, We kneel before YHWH our Maker.
Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
7 For He [is] our God, and we the people of His pasture, And the flock of His hand, Today, if you listen to His voice,
gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
8 Do not harden your heart as [in] Meribah, As [in] the day of Massah in the wilderness,
“Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
9 Where your fathers have tried Me, Have proved Me, indeed, have seen My work.
inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
10 Forty years I am weary of the generation, And I say, “A people erring in heart—they! And they have not known My ways”:
Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
11 Where I swore in My anger, “If they come into My rest—!”
Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”

< Psalms 95 >