< Psalms 91 >
1 He who is dwelling In the secret place of the Most High, Habitually lodges in the shade of the Mighty,
Shi wanda yake zama a wurin Mafi Ɗaukaka zai huta a cikin inuwar Maɗaukaki.
2 He is saying of YHWH, “My refuge, and my bulwark, my God, I trust in Him,”
Zan ce game da Ubangiji, “Shi ne mafakata da kagarata, Allahna, wanda nake dogara.”
3 For He delivers you from the snare of a fowler, From a calamitous pestilence.
Tabbatacce zai cece ka daga tarkon mai farauta da kuma daga cututtuka masu kisa.
4 He covers you over with His pinion, And under His wings you trust, His truth [is] a shield and buckler.
Zai rufe ka da fikafikansa, a ƙarƙashin fikafikansa kuwa za ka sami mafaka; amincinsa zai zama maka garkuwa da katanga.
5 You are not afraid of fear by night, Of arrow that flies by day,
Ba za ka ji tsoron razanar dare, ko kibiyoyi da suke firiya da rana ba,
6 Of pestilence that walks in thick darkness, Of destruction that destroys at noon,
ko bala’in da yake aukowa cikin duhu, ko annobar da take hallakarwa da tsakar rana.
7 One thousand fall at your side, And a myriad at your right hand, [But] it does not come near to you.
Dubu za su iya fāɗuwa a gefenka, dubu goma a hannun damanka, amma ba abin da zai zo kusa da kai.
8 But with your eyes you look, And you see the reward of the wicked,
Za ka dai gan da idanunka yadda ake hukunta mugaye.
9 (For You, O YHWH, [are] my refuge), You made the Most High your habitation.
In ka mai da Mafi Ɗaukaka wurin zamanka, har ma Ubangiji wanda yake mafakata,
10 Evil does not happen to you, And a plague does not come near your tent,
to, babu wani mugun abin da zai same ka, ba masifar da za tă zo kusa da tentinka.
11 For He charges His messengers for you, To keep you in all your ways,
Gama zai umarci mala’ikunsa game da kai don su tsare ka a dukan hanyoyinka;
12 On the hands they bear you up, Lest you strike your foot against a stone.
za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.
13 You tread on lion and cobra, You trample young lion and dragon.
Za ka taka zaki da gamsheƙa; za ka tattake babban zaki da maciji.
14 Because he has delighted in Me, I also deliver him—I set him on high, Because he has known My Name.
Ubangiji ya ce, “Domin ya ƙaunace ni, zan kuɓutar da shi; zan kiyaye shi, gama ya yarda da sunana.
15 He calls Me, and I answer him, I [am] with him in distress, I deliver him, and honor him.
Zai kira bisa sunana, zan kuma amsa masa; zan kasance tare da shi a lokacin wahala, zan kuɓutar da shi in kuma girmama shi.
16 I satisfy him with [the] length of [his] days, And I cause him to look on My salvation!
Da tsawon rai zan ƙosar da shi in kuma nuna masa cetona.”