< Psalms 73 >

1 A PSALM OF ASAPH. Surely God [is] good to Israel, to the clean of heart. And I—as a little thing, My feet have been turned aside,
Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
2 As nothing, my steps have slipped, For I have been envious of the boastful,
Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
3 I see the peace of the wicked, That there are no bands at their death,
Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
4 And their might [is] firm.
Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
5 They are not in the misery of mortals, And they are not plagued with common men.
Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
6 Therefore pride has encircled them, Violence covers them as a dress.
Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
7 Their eye has come out from fat. The imaginations of the heart transgressed;
Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
8 They do corruptly, And they speak in the wickedness of oppression, They speak from on high.
Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
9 They have set their mouth in the heavens, And their tongue walks in the earth.
Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
10 Therefore His people return here, And waters of fullness are wrung out to them.
Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
11 And they have said, “How has God known? And is there knowledge in the Most High?”
Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
12 Behold, these [are] the wicked and easy ones of the age, They have increased strength.
Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
13 Only—a vain thing! I have purified my heart, And I wash my hands in innocence,
Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
14 And I am plagued all the day, And my reproof—every morning.
Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
15 If I have said, “I recount thus,” Behold, I have deceived a generation of Your sons.
Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
16 And I think to know this, It [is] perverseness in my eyes,
Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
17 Until I come into the sanctuaries of God, I attend to their latter end.
sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
18 Surely You set them in slippery places, You have caused them to fall to desolations.
Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
19 How they have become a desolation as in a moment, They have been ended—consumed from terrors.
Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
20 As a dream from awakening, O Lord, In awaking, You despise their image.
Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
21 For my heart shows itself violent, And my reins prick themselves,
Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
22 And I am brutish, and do not know. I have been a beast with You.
na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
23 And I [am] continually with You, You have laid hold on my right hand.
Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
24 You lead me with Your counsel, And after, receive me [to] glory.
Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
25 Whom do I have in the heavens? And none have I desired in earth [besides] You.
Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
26 My flesh and my heart have been consumed, God [is] the rock of my heart and my portion for all time.
Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
27 For behold, those far from You perish, You have cut off everyone, Who is going whoring from You.
Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
28 And [the] nearness of God to me [is] good, I have placed my refuge in Lord YHWH, To recount all Your works!
Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.

< Psalms 73 >