< Psalms 62 >
1 TO THE OVERSEER. FOR JEDUTHUN. A PSALM OF DAVID. Toward God alone [is] my soul silent, My salvation [is] from Him.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zaburar Dawuda. Raina na samun hutu a wurin Allah ne kaɗai; cetona na zuwa daga gare shi.
2 He alone [is] my rock, and my salvation, My tower, I am not much moved.
Shi kaɗai ne dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
3 Until when do you devise mischief against a man? All of you are destroyed, As a wall inclined, a hedge that is cast down.
Har yaushe za ku tasar wa mutum guda? Dukanku ne za ku kā da shi wannan jinganannen bango, wannan rusasshen katanga?
4 Only—from his excellence They have consulted to drive away, They enjoy a lie, they bless with their mouth, And revile with their heart. (Selah)
Sun kintsa sosai su tumɓuke shi daga matsayinsa mai martaba; suna jin daɗi yin ƙarairayi. Sukan sa wa mutum albarka da bakinsu, amma a zuciyarsu la’antawa suke yi. (Sela)
5 For God alone, be silent, O my soul, For my hope [is] from Him.
Ka nemi hutu, ya raina, a wurin Allah kaɗai; dogarata kan zo daga gare shi ne.
6 He alone [is] my rock and my salvation, My tower, I am not moved.
Shi ne kaɗai dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
7 On God [is] my salvation, and my glory, The rock of my strength, my refuge [is] in God.
Cetona da girmata sun dangana ga Allah ne, shi ne dutsena mai ƙarfi, mafakata.
8 Trust in Him at all times, O people, Pour forth your heart before Him, God [is] a refuge for us. (Selah)
Ku dogara a gare shi a duk lokuta, ya mutane; ku faɗi albarkaci bakin zukatanku a gare shi, gama Allah ne mafakarmu. (Sela)
9 Surely vanity the low, a lie the high. In balances to go up They [are] lighter than a breath.
Talakawa dai kamar shaƙar iska suke, Attajirai dai kamar shirim suke; in aka auna a ma’auni, su ba wani abu ba ne; dukansu dai kamar shaƙar iska ne kawai.
10 Do not trust in oppression, And do not become vain in robbery, Do not set the heart [on] wealth when it increases.
Kada ku dogara a kan ƙwace ko yin fariya a kayan sata; ko arzikinku ya ƙaru, kada ku sa zuciyarku a kansu.
11 Once has God spoken, twice I heard this, That “strength [is] with God.”
Abu guda Allah ya ce, abubuwa biyu na ji, “Cewa kai, ya Allah, kake mai ƙarfi,
12 And with You, O Lord, [is] kindness, For You repay to each, According to his work!
kuma cewa kai, ya Ubangiji, mai ƙauna ne. Tabbatacce za ka sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya yi.”