< Psalms 51 >

1 TO THE OVERSEER. A PSALM OF DAVID, IN THE COMING OF NATHAN THE PROPHET TO HIM WHEN HE HAS GONE IN TO BATHSHEBA. Favor me, O God, according to Your kindness, According to the abundance of Your mercies, Blot out my transgressions.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
2 Thoroughly wash me from my iniquity, And cleanse me from my sin,
Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
3 For I know my transgressions, And my sin [is] continually before me.
Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
4 Against You, You only, I have sinned, And done evil in Your eyes, So that You are righteous in Your words, You are pure in Your judging.
Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
5 Behold, I have been brought forth in iniquity, And my mother conceives me in sin.
Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
6 Behold, You have desired truth in the inward parts, And in the hidden part You cause me to know Wisdom.
Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
7 You cleanse me with hyssop and I am clean, Wash me, and I am whiter than snow.
Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
8 You cause me to hear joy and gladness, You make bones You have bruised joyful.
Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
9 Hide Your face from my sin. And blot out all my iniquities.
Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
10 Create for me a clean heart, O God, And renew a right spirit within me.
Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
11 Do not cast me forth from Your presence, And do not take Your Holy Spirit from me.
Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
12 Restore to me the joy of Your salvation, And a willing spirit sustains me.
Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
13 I teach transgressors Your ways, And sinners return to You.
Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
14 Deliver me from blood, O God, God of my salvation, My tongue sings of Your righteousness.
Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
15 O Lord, you open my lips, And my mouth declares Your praise.
Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
16 For You do not desire sacrifice, or I give [it], You do not accept burnt-offering.
Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
17 The sacrifices of God [are] a broken spirit, A heart broken and bruised, O God, You do not despise.
Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
18 Do good in Your good pleasure with Zion, You build the walls of Jerusalem.
Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
19 Then You desire sacrifices of righteousness, Burnt-offering, and whole burnt-offering, Then they offer bullocks on your altar!
Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.

< Psalms 51 >