< Psalms 44 >

1 TO THE OVERSEER. AN INSTRUCTION OF THE SONS OF KORAH. O God, we have heard with our ears, Our fathers have recounted to us, The work You worked in their days, In the days of old.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
2 You, [with] Your hand, have dispossessed nations. And You plant them. You afflict peoples, and send them away.
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
3 For they did not possess the land by their sword, And their arm did not give salvation to them, But Your right hand, and Your arm, And the light of Your countenance, Because You had accepted them.
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
4 You [are] He, my King, O God, Command the deliverances of Jacob.
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
5 By You we push our adversaries, By Your Name we tread down our withstanders,
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
6 For I do not trust in my bow, And my sword does not save me.
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
7 For You have saved us from our adversaries, And You have put to shame those hating us.
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
8 In God we have boasted all the day, And we thank Your Name for all time. (Selah)
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
9 In anger You have cast off and cause us to blush, And do not go forth with our hosts.
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
10 You cause us to turn backward from an adversary, And those hating us, Have spoiled for themselves.
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
11 You make us food like sheep, And You have scattered us among nations.
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
12 You sell Your people—without wealth, And have not become great by their price.
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
13 You make us a reproach to our neighbors, A scorn and a reproach to our surrounders.
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
14 You make us an allegory among nations, A shaking of the head among peoples.
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
15 All the day my confusion [is] before me, And the shame of my face has covered me.
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
16 Because of the voice of a reproacher and reviler, Because of an enemy and a self-avenger.
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
17 All this met us, and we did not forget You, Nor have we dealt falsely in Your covenant.
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
18 We do not turn our heart backward, Nor turn aside our step from Your path.
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
19 But You have struck us in a place of dragons, And cover us over with death-shade.
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
20 If we have forgotten the Name of our God, And spread our hands to a strange God,
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
21 Does God not search this out? For He knows the secrets of the heart.
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
22 Surely, for Your sake we have been slain all the day, Reckoned as sheep of the slaughter.
Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
23 Stir up—why do You sleep, O Lord? Awake, do not cast us off forever.
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
24 Why do You hide Your face? You forget our afflictions and our oppression,
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
25 For our soul has bowed to the dust, Our belly has cleaved to the earth.
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
26 Arise, a help to us, And ransom us for your kindness’ sake.
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.

< Psalms 44 >