< Psalms 39 >

1 TO THE OVERSEER. FOR JEDUTHUN. A PSALM OF DAVID. I have said, “I observe my ways, Against sinning with my tongue, I keep a curb for my mouth, While the wicked [is] before me.”
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zabura ta Dawuda. Na ce, “Zan lura da hanyoyina zan kuma kiyaye harshena daga zunubi; zan sa linzami a bakina muddin mugaye suna a gabana.”
2 I was mute [with] silence, I kept silent from good, and my pain is excited.
Na yi shiru, ban ce kome ba, Ko a kan abin da yake da kyau! Amma duk da haka wahalata sai ƙaruwa take yi;
3 My heart [is] hot within me, In my meditating the fire burns, I have spoken with my tongue.
zuciyata ta ƙara zafi a cikina. Kuma sa’ad da nake tunani, wuta ta yi ta kuna; sai na yi magana da harshena na ce,
4 “Cause me to know, O YHWH, my end, And the measure of my days—what it [is],” I know how frail I [am].
“Nuna mini, ya Ubangiji, ƙarshen rayuwata da kuma yawan kwanakina; bari in san yadda rayuwata tana wucewa da sauri.
5 Behold, You have made my days handbreadths, And my age [is] as nothing before You, Only, every man set up [is] all vanity. (Selah)
Ka sa kwanakina suka zama tafin hannu ne kawai; yawan shekaruna kamar ba kome ba ne a gabanka. Duk ran mutum shaƙar iska ne kurum, har ma waɗanda suke tsammani suke da kāriya. (Sela)
6 Only, each habitually walks in an image, Only, [in] vain, they are disquieted, He heaps up and does not know who gathers them.
“Mutum dai shirim ne kawai yayinda yake kai da komowa. Yana ta yawo, amma a banza ne kawai; yakan tara dukiya, ba tare da sanin wa zai more ta ba.
7 And now, what have I expected? O Lord, my hope—it [is] of You.
“Amma yanzu, ya Ubangiji, me zan nema? Begena yana a gare ka.
8 Deliver me from all my transgressions, Do not make me a reproach of the fool.
Ka cece ni daga dukan laifofina; kada ka sa in zama abin dariya ga wawaye.
9 I have been mute, I do not open my mouth, Because You have done [it].
Na yi shiru; ba zan buɗe bakina ba, gama kai ne wanda ka aikata wannan.
10 Turn aside Your stroke from off me, From the striving of Your hand I have been consumed.
Ka ɗauke bulalarka daga gare ni; na ji jiki ta wurin bugun da hannunka ya yi mini.
11 With reproofs against iniquity, You have corrected man, And dissolve his desirableness as a moth, Only, every man [is] vanity. (Selah)
Kakan tsawata ka kuma hore mutane saboda zunubinsu; kakan cinye wadatarsu kamar yadda asu ke yi, kowane mutum dai shaƙar iska ne. (Sela)
12 Hear my prayer, O YHWH, And give ear [to] my cry, Do not be silent to my tear, For I [am] a sojourner with You, A settler like all my fathers.
“Ka ji addu’ata, ya Ubangiji, ka saurari kukata ta neman taimako; kada ka kurmance ga kukata. Gama ina zama tare da kai kamar baƙo, baƙo, kamar yadda dukan kakannina sun kasance.
13 Look from me, and I brighten up before I go and am not!
Ka kau da fuskarka daga gare ni, saboda in sāke yin farin ciki kafin in tafi in kuma rabu da nan.”

< Psalms 39 >