< Psalms 3 >
1 A PSALM OF DAVID, IN HIS FLEEING FROM THE FACE OF HIS SON ABSALOM. YHWH, how my distresses have multiplied! Many are rising up against me.
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
2 Many are saying of my soul, “There is no salvation for him in God.” (Selah)
Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
3 And You, O YHWH, [are] a shield for me, My glory, and lifter up of my head.
Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
4 My voice [is] to YHWH: I call and He answers me from His holy hill, (Selah)
Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
5 I have lain down, and I sleep, I have awoken, for YHWH sustains me.
Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
6 I am not afraid of myriads of people, That they have set against me all around.
Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
7 Rise, O YHWH! Save me, my God! For You have struck all my enemies [on] the cheek. You have broken the teeth of the wicked.
Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
8 This salvation [is] of YHWH; Your blessing [is] on Your people! (Selah)
Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)