< Psalms 27 >
1 BY DAVID. YHWH [is] my light and my salvation, Whom do I fear? YHWH [is] the strength of my life, Of whom am I afraid?
Ta Dawuda. Ubangiji ne haskena da cetona, wa zan ji tsoro? Ubangiji ne mafakar raina, wane ne zan ji tsoro?
2 When evildoers come near to me to eat my flesh, My adversaries and my enemies to me, They have stumbled and fallen.
Sa’ad da mugaye suka tasar mini don su cinye ni, sa’ad da abokan gābana da maƙiyina suka kawo mini hari, sun yi tuntuɓe suka fāɗi.
3 Though a host encamps against me, My heart does not fear, Though war rises up against me, In this I [am] confident.
Ko da yake mayaƙa sun kewaye ni, zuciyata ba za tă ji tsoro ba; ko da yake ya ɓarke a kaina, duk da haka zan ƙarfafa.
4 One [thing] I asked of YHWH—it I seek: My dwelling in the house of YHWH, All the days of my life, To look on the pleasantness of YHWH, And to inquire in His temple.
Abu guda na roƙi Ubangiji, wannan shi ne na nema, cewa in zauna a gidan Ubangiji dukan kwanakin raina, in dubi kyan Ubangiji in kuma neme shi a cikin haikalinsa.
5 For He hides me in a dwelling place in the day of evil, He hides me in a secret place of His tent, He raises me up on a rock.
Gama a lokacin wahala, zai kiyaye ni lafiya a wurin zamansa; zai ɓoye ni cikin inuwar tabanakul nasa ya kuma sa ni can a bisa dutse.
6 And now my head is lifted up, Above my enemies—my surrounders, And I sacrifice in His tent sacrifices of shouting, I sing, indeed, I sing praise to YHWH.
Sa’an nan kaina zai ɗaukaka a bisa abokan gābana waɗanda suka kewaye ni; a tabanakul nasa zan miƙa hadaya da sowa ta farin ciki; zan rera in kuma yi kiɗi ga Ubangiji.
7 Hear, O YHWH, my voice—I call, And favor me, and answer me.
Ka ji muryata sa’ad da na yi kira, ya Ubangiji; ka yi mini jinƙai ka kuma amsa mini.
8 My heart said to You, “They sought my face, Your face, O YHWH, I seek.”
Zuciyata kan faɗa game da kai, “Nemi fuskarsa!” Fuskarka, Ubangiji, zan nema.
9 Do not hide Your face from me, Do not turn Your servant aside in anger, You have been my help. Do not leave me, nor forsake me, O God of my salvation.
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni, kada ka kore bawanka daga gare ka cikin fushi; kai ne ka kasance mai taimakona. Kada ka ƙi ni ko ka yashe ni, Ya Allah Mai cetona.
10 When my father and my mother Have forsaken me, then YHWH gathers me.
Ko da mahaifina da mahaifiyata sun yashe ni, Ubangiji zai karɓe ni.
11 Show me, O YHWH, Your way, And lead me in a path of uprightness, For the sake of my beholders.
Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji; ka bi da ni a miƙaƙƙiyar hanya saboda masu danne ni.
12 Do not give me to the will of my adversaries, For false witnesses have risen against me, And they breathe out violence to me.
Kada ka ba da ni da sha’awar maƙiyina, gama masu shaidar ƙarya sun taso a kaina, suna numfasa tashin hankali.
13 I had not believed to look on the goodness of YHWH In the land of the living!
Har yanzu ina da ƙarfin gwiwa a wannan cewa zan ga alherin Ubangiji; a ƙasar masu rai.
14 Look to YHWH—be strong, And He strengthens your heart, Indeed, look to YHWH!
Ka dogara ga Ubangiji, ka yi ƙarfin hali ka yi ƙarfin zuciya ka kuma dogara ga Ubangiji.