< Psalms 18 >
1 TO THE OVERSEER. BY A SERVANT OF YHWH, BY DAVID, WHO HAS SPOKEN TO YHWH THE WORDS OF THIS SONG IN THE DAY YHWH DELIVERED HIM FROM THE HAND OF ALL HIS ENEMIES, AND FROM THE HAND OF SAUL, AND HE SAYS: I love You, O YHWH, my strength.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
2 YHWH [is] my rock, and my bulwark, And my deliverer, My God [is] my rock, I trust in Him: My shield, and the horn of my salvation, My high tower.
Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
3 I call on YHWH, the Praised One, And I am saved from my enemies.
Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
4 Cords of death have surrounded me, And streams of the worthless make me afraid.
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
5 Cords of Sheol have surrounded me, Snares of death have been before me. (Sheol )
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
6 In my adversity I call YHWH, And I cry to my God. He hears my voice from His temple, And My cry comes into His ears before Him.
Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
7 And the earth shakes and trembles, And foundations of hills are troubled, And they shake—because He has wrath.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
8 Smoke has gone up from His nostrils, And fire from His mouth consumes, Coals have been kindled by it.
Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
9 And He inclines the heavens, and comes down, And thick darkness [is] under His feet.
Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
10 And He rides on a cherub, and flies, And He flies on wings of wind.
Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
11 He makes darkness His secret place, Around Him His dwelling place, Darkness of waters, thick clouds of the skies.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
12 From the brightness before Him His thick clouds have passed on, Hail and coals of fire.
daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
13 And YHWH thunders in the heavens, And the Most High gives forth His voice, Hail and coals of fire.
Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
14 And He sends His arrows and scatters them, And much lightning, and crushes them.
Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
15 And the streams of waters are seen, And foundations of the earth are revealed, From Your rebuke, O YHWH, From the breath of the wind of Your anger.
Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
16 He sends from above—He takes me, He draws me out of many waters.
Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
17 He delivers me from my strong enemy, And from those hating me, For they have been stronger than I.
Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
18 They go before me in a day of my calamity And YHWH is for a support to me.
Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
19 And He brings me forth to a large place, He draws me out, because He delighted in me.
Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
20 YHWH repays me According to my righteousness, According to the cleanness of my hands, He returns to me.
Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
21 For I have kept the ways of YHWH, And have not done wickedly against my God.
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
22 For all His judgments [are] before me, And I do not turn His statutes from me.
Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
23 And I am perfect with Him, And I keep myself from my iniquity.
Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
24 And YHWH returns to me, According to my righteousness, According to the cleanness of my hands, Before His eyes.
Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
25 With the kind You show Yourself kind, With a perfect man You show Yourself perfect.
Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
26 With the pure You show Yourself pure, And with the perverse You show Yourself a wrestler,
ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
27 For You save a poor people, And cause the eyes of the high to fall.
Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
28 For You light my lamp, My God YHWH enlightens my darkness.
Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
29 For by You I run [against] a troop! And by my God I leap a wall.
Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
30 God—perfect [is] His way, The saying of YHWH is tried, He [is] a shield to all those trusting in Him.
Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
31 For who [is] God besides YHWH? And who [is] a rock except our God?
Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
32 God—who is girding me [with] strength, And He makes my way perfect.
Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
33 Making my feet like does, And on my high places causes me to stand.
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
34 Teaching my hands for battle, And a bow of bronze was brought down by my arms.
Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
35 And You give to me the shield of Your salvation, And Your right hand supports me, And Your lowliness makes me great.
Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
36 You enlarge my step under me, And my ankles have not slipped.
Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
37 I pursue my enemies, and overtake them, And do not turn back until they are consumed.
Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
38 I strike them, and they are not able to rise, They fall under my feet,
Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
39 And You gird me [with] strength for battle, You cause my withstanders to bow under me.
Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
40 As for my enemies—You have given to me the neck, As for those hating me—I cut them off.
Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
41 They cry, and there is no savior, On YHWH, and He does not answer them.
Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
42 And I beat them as dust before wind, I empty them out as mire of the streets.
Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
43 You deliver me From the strivings of the people, You place me for a head of nations, A people I have not known serve me.
Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
44 At the hearing of the ear they listen to me, Sons of a stranger feign obedience to me,
da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
45 Sons of a stranger fade away, And are slain out of their close places.
Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
46 YHWH lives—and blessed [is] my rock, And exalted is the God of my salvation.
Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
47 God—who is giving vengeance to me, And He subdues peoples under me,
Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
48 My deliverer from my enemies, You raise me above my withstanders, Deliver me from a man of violence.
wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
49 Therefore I confess You among nations, O YHWH, And I sing praise to Your Name,
Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
50 Magnifying the salvation of His king, And doing kindness to His anointed, To David, and to his seed—for all time!
Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.