< Psalms 147 >

1 Praise YAH! For [it is] good to praise our God, For pleasant—lovely [is] praise.
Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
2 YHWH [is] building Jerusalem, He gathers the driven away of Israel.
Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
3 Who is giving healing to the broken of heart, And is binding up their griefs.
Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
4 Appointing the number of the stars, He gives names to all of them.
Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
5 Our Lord [is] great, and abundant in power, There is no narration of His understanding.
Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
6 YHWH is causing the meek to stand, Making the wicked low to the earth.
Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
7 Answer to YHWH with thanksgiving, Sing to our God with a harp.
Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
8 Who is covering the heavens with clouds, Who is preparing rain for the earth, Who is causing grass to spring up [on] mountains,
Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
9 Giving to the beast its food, To the young of the ravens that call.
Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
10 He does not delight in the might of the horse, He is not pleased in the legs of a man.
Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
11 YHWH is pleased with those fearing Him, With those waiting for His kindness.
Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
12 Glorify, O Jerusalem, YHWH, Praise your God, O Zion.
Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
13 For He strengthened the bars of your gates, He has blessed your sons in your midst.
Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
14 Who is making your border peace, He satisfies you [with] the fat of wheat.
Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
15 Who is sending forth His saying [on] earth, His word runs very speedily.
Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
16 Who is giving snow like wool, He scatters hoarfrost as ashes.
Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
17 Casting forth His ice like morsels, Who stands before His cold?
Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
18 He sends forth His word and melts them, He causes His wind to blow—the waters flow.
Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
19 Declaring His words to Jacob, His statutes and His judgments to Israel.
Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
20 He has not done so to any nation, As for judgments, they have not known them. Praise YAH!
Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.

< Psalms 147 >