< Psalms 122 >

1 A SONG OF THE ASCENTS. BY DAVID. I have rejoiced in those saying to me, “We go to the house of YHWH.”
Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
2 Our feet have been standing in your gates, O Jerusalem!
Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
3 Jerusalem—the built one—[Is] as a city that is joined to itself together.
An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
4 For there tribes have gone up, Tribes of YAH, companies of Israel, To give thanks to the Name of YHWH.
A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
5 For there thrones of judgment have sat, Thrones of the house of David.
A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
6 Ask [for] the peace of Jerusalem, Those loving you are at rest.
Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
7 Peace is in your bulwark, rest in your high places,
Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
8 For the sake of my brothers and my companions, Please let me speak, “Peace [be] in you.”
Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
9 For the sake of the house of our God YHWH, I seek good for you!
Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.

< Psalms 122 >