< Psalms 108 >
1 A SONG. A PSALM OF DAVID. My heart is prepared, O God, I sing, indeed, I sing praise, also my glory.
Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
2 Awake, stringed instrument and harp, I awake the dawn.
Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
3 I thank You among peoples, O YHWH, And I praise You among the nations.
Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
4 For Your kindness [is] great above the heavens, And Your truth to the clouds.
Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
5 Be exalted above the heavens, O God, And Your glory above all the earth.
A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
6 That Your beloved ones may be delivered, Save [with] Your right hand, and answer us.
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
7 God has spoken in His holiness: I exult, I apportion Shechem, And I measure the Valley of Succoth,
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
8 Gilead [is] Mine, Manasseh [is] Mine, And Ephraim [is] the strength of My head, Judah [is] My lawgiver,
Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
9 Moab [is] a pot for My washing, On Edom I cast My shoe, Over Philistia I habitually shout.
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
10 Who brings me [into] the fortified city? Who has led me to Edom?
Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
11 Have You not, O God, cast us off? And You do not go out, O God, with our hosts!
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
12 Give to us help from adversity, And the salvation of man is vain.
Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
13 We do mightily in God, And He treads down our adversaries!
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.