< Psalms 107 >

1 “Give thanks to YHWH, For [He is] good, for His kindness [is] for all time”:
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Let the redeemed of YHWH say [so], Whom He redeemed from the hand of an adversary.
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 And has gathered them from the lands, From east and from west, From north, and from the sea.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 They wandered in a wilderness, in a desert by the way, They have not found a city of habitation.
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 Hungry—indeed—thirsty, Their soul becomes feeble in them,
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 And they cry to YHWH in their adversity, He delivers them from their distress,
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 And causes them to tread in a right way, To go to a city of habitation.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 They confess to YHWH His kindness, And His wonders to the sons of men.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 For He has satisfied a longing soul, And has filled a hungry soul [with] goodness.
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 Inhabitants of dark places and death-shade, Prisoners of affliction and of iron,
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 Because they changed the saying of God, And despised the counsel of the Most High.
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 And He humbles their heart with labor, They have been feeble, and there is no helper.
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 And they cry to YHWH in their adversity, He saves them from their distresses.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 He brings them out from the dark place, And death-shade, And He draws away their bands.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 They confess to YHWH His kindness, And His wonders to the sons of men.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 For He has broken doors of bronze, And He has cut bars of iron.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 Fools, by means of their transgression, And by their iniquities, afflict themselves.
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 Their soul detests all food, And they come near to the gates of death,
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 And cry to YHWH in their adversity, He saves them from their distresses,
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 He sends His word and heals them, And delivers [them] from their destructions.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 They confess to YHWH His kindness, And His wonders to the sons of men,
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 And they sacrifice sacrifices of thanksgiving, And recount His works with singing.
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 Those going down [to] the sea in ships, Doing business in many waters,
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 They have seen the works of YHWH, And His wonders in the deep.
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 And He commands, and appoints a storm, And it lifts up its billows,
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 They go up [to] the heavens, they go down [to] the depths, Their soul is melted in evil.
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 They reel to and fro, and move as a drunkard, And all their wisdom is swallowed up.
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 And they cry to YHWH in their adversity, And He brings them out from their distresses.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 He calms a whirlwind, And their billows are hushed.
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 And they rejoice because they are quiet, And He leads them to the haven of their desire.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 They confess to YHWH His kindness, And His wonders to the sons of men,
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 And they exalt Him in [the] assembly of [the] people, And praise Him in [the] seat of [the] elderly.
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 He makes rivers become a wilderness, And fountains of waters become dry land.
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 A fruitful land becomes a barren place, For the wickedness of its inhabitants.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 He makes a wilderness become a pool of water, And a dry land become fountains of waters.
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 And He causes the hungry to dwell there, And they prepare a city of habitation.
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 And they sow fields, and plant vineyards, And they make fruits of increase.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 And He blesses them, and they multiply exceedingly, And He does not diminish their livestock.
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 And they are diminished, and bow down, By restraint, evil, and sorrow.
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 He is pouring contempt on nobles, And causes them to wander in vacancy—no way.
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 And sets the needy on high from affliction, And places families as a flock.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 The upright see and rejoice, And all perversity has shut her mouth.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Who [is] wise, and observes these? They understand the kind acts of YHWH!
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.

< Psalms 107 >