< Psalms 105 >

1 Give thanks to YHWH—call on His Name, Make His acts known among the peoples.
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
2 Sing to Him—sing praise to Him, Meditate on all His wonders.
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
3 Boast yourselves in His Holy Name, The heart of those seeking YHWH rejoices.
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
4 Seek YHWH and His strength, Seek His face continually.
Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
5 Remember His wonders that He did, His signs and the judgments of His mouth.
Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
6 O seed of Abraham, His servant, O sons of Jacob, His chosen ones.
Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
7 He [is] our God YHWH, His judgments [are] in all the earth.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
8 He has remembered His covenant for all time, The word He commanded to one thousand generations,
Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
9 That He has made with Abraham, And His oath to Isaac,
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
10 And establishes it to Jacob for a statute, To Israel—a perpetual covenant,
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
11 Saying, “I give the land of Canaan to you, The portion of your inheritance,”
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
12 In their being few in number, But a few, and sojourners in it.
Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
13 And they go up and down, from nation to nation, From a kingdom to another people.
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
14 He has not permitted any to oppress them And He reproves kings for their sakes.
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
15 “Do not strike against My anointed, And do no evil to My prophets.”
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
16 And He calls a famine on the land, He has broken the whole staff of bread.
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
17 He has sent a man before them, Joseph has been sold for a servant.
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
18 They have afflicted his feet with chains, Iron has entered his soul,
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
19 Until the time of the coming of His word The saying of YHWH has tried him.
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
20 The king has sent, and looses him, The ruler of the peoples, and draws him out.
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
21 He has made him lord of his house, And ruler over all his possessions.
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
22 To bind his chiefs at his pleasure, And he makes his elderly wise.
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
23 And Israel comes into Egypt, And Jacob has sojourned in the land of Ham.
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
24 And He makes His people very fruitful, And makes it mightier than its adversaries.
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
25 He turned their heart to hate His people, To conspire against His servants.
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
26 He has sent His servant Moses, Aaron whom He had fixed on.
Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
27 They have set among them the matters of His signs, And wonders in the land of Ham.
Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
28 He has sent darkness, and it is dark, And they have not provoked His word.
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
29 He has turned their waters to blood, And puts their fish to death.
Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
30 Their land has teemed [with] frogs, In the inner chambers of their kings.
Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
31 He has commanded, and the beetle comes, Lice into all their border.
Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
32 He has made their showers hail, A flaming fire [is] in their land.
Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
33 And He strikes their vine and their fig, And shatters the trees of their border.
ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
34 He has commanded, and the locust comes, And the cankerworm—innumerable,
Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
35 And it consumes every herb in their land, And it consumes the fruit of their ground.
suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
36 And He strikes every firstborn in their land, The first-fruit of all their strength,
Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
37 And brings them out with silver and gold, And there is not a feeble one in its tribes.
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
38 Egypt has rejoiced in their going forth, For their fear had fallen on them.
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
39 He has spread a cloud for a covering, And fire to enlighten the night.
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
40 They have asked, and He brings quails, And satisfies them [with] bread of the heavens.
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
41 He has opened a rock, and waters flow, They have gone on in dry places—a river.
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
42 For He has remembered His holy word, With His servant Abraham,
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
43 And He brings forth His people with joy, His chosen ones with singing.
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
44 And He gives to them the lands of nations, And they possess the labor of peoples,
ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
45 That they may observe His statutes, And may keep His laws. Praise YAH!
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.

< Psalms 105 >