< Psalms 103 >
1 BY DAVID. Bless, O my soul, YHWH, And all my inward parts—His Holy Name.
Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
2 Bless, O my soul, YHWH, And do not forget all His benefits,
Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
3 Who is forgiving all your iniquities, Who is healing all your diseases,
wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
4 Who is redeeming your life from destruction, Who is crowning you [with] kindness and mercies,
wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
5 Who is satisfying your desire with good, Your youth renews itself as an eagle.
Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
6 YHWH is doing righteousness and judgments For all the oppressed.
Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
7 He makes His ways known to Moses, His acts to the sons of Israel.
Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
8 YHWH [is] merciful and gracious, Slow to anger, and abundant in mercy.
Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
9 He does not strive forever, Nor does He watch for all time.
Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
10 He has not done to us according to our sins, Nor according to our iniquities Has He conferred benefits on us.
ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
11 For as the height of the heavens [is] above the earth, His kindness has been mighty over those fearing Him.
Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
12 He has put our transgressions far from us—as the distance of east from west.
kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
13 As a father has mercy on sons, YHWH has mercy on those fearing Him.
Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
14 For He has known our frame, Remembering that we [are] dust.
gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
15 Mortal man! His days [are] as grass, He flourishes as a flower of the field;
Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
16 For a wind has passed over it, and it is not, And its place does not discern it anymore.
iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
17 And the kindness of YHWH [Is] from age even to age on those fearing Him, And His righteousness to sons’ sons,
Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
18 To those keeping His covenant, And to those remembering His precepts to do them.
tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
19 YHWH has established His throne in the heavens, And His kingdom has ruled over all.
Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
20 Bless YHWH, you His messengers, Mighty in power—doing His word, To listen to the voice of His word.
Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
21 Bless YHWH, all you His hosts, His ministers—doing His pleasure.
Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
22 Bless YHWH, all you His works, In all places of His dominion. Bless, O my soul, YHWH!
Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.