< Proverbs 9 >
1 Wisdom has built her house, She has hewn out her pillars—seven.
Hikima ta gina gidanta; ta yi ginshiƙansa bakwai.
2 She has slaughtered her slaughter, She has mingled her wine, Indeed, she has arranged her table.
Ta shirya abincinta gauraye da ruwan inabinta; ta kuma shirya teburinta.
3 She has sent forth her girls, She cries on the tops of the high places of the city:
Ta aiki bayinta mata, tana kuma kira daga wurare masu tsayi na birnin.
4 “Who [is] simple? Let him turn aside here.” Whoever lacks heart: she has said to him,
“Bari dukan waɗanda suke marasa azanci su zo nan ciki!” Tana faɗa wa marasa hankali.
5 “Come, eat of my bread, And drink of the wine I have mingled.
“Ku zo, ku ci abincina da ruwan inabin da na gauraye.
6 Forsake the simple and live, And be blessed in the way of understanding.”
Ku bar hanyoyinku marasa hankali za ku kuwa rayu; yi tafiya a hanyar fahimi.
7 The instructor of a scorner Is receiving for it—shame, And a reprover of the wicked—his blemish.
“Duk wanda ya yi wa mai ba’a gyara yana gayyatar zagi duk wanda ya tsawata wa mugu yakan gamu da cin mutunci.
8 Do not reprove a scorner, lest he hate you, Give reproof to the wise, and he loves you.
Kada ka tsawata wa masu ba’a gama za su ƙi ka; ka tsawata wa mai hikima zai kuwa ƙaunace ka.
9 Give to the wise, and he is wiser still, Make known to the righteous, And he increases learning.
Ka koya wa mai hikima zai kuwa ƙara hikima; ka koya wa mai adalci zai kuwa ƙara koyonsa.
10 The commencement of wisdom [is] the fear of YHWH, And a knowledge of the Holy Ones [is] understanding.
“Tsoron Ubangiji shi ne mafarin hikima, sanin Mai Tsarki kuwa fahimi ne.
11 For by me your days multiply, And years of life are added to you.
Gama ta wurina kwanakinka za su yi yawa, za a kuwa ƙara wa ranka shekaru.
12 If you have been wise, you have been wise for yourself, And you have scorned—you bear [it] alone.
In kana da hikima, hikimarka za tă ba ka lada; in kai mai ba’a ne, kai kaɗai za ka sha wahala.”
13 A foolish woman [is] noisy, Simple, and has not known what.
Wawancin mace a bayyane yake; ba ta da ɗa’a kuma ba ta da sani.
14 And she has sat at the opening of her house, On a throne—the high places of the city,
Takan zauna a ƙofar gidanta, a wurin zama a wurin mafi tsayi na birni,
15 To call to those passing by the way, Who are going straight [on] their paths.
tana kira ga masu wucewa, waɗanda suke tafiya kai tsaye a hanyarsu.
16 “Who [is] simple? Let him turn aside here.” And whoever lacks heart—she said to him,
“Bari dukan waɗanda suke marasa azanci su zo cikin nan!” Tana ce wa marasa hankali.
17 “Stolen waters are sweet, And hidden bread is pleasant.”
“Ruwan da aka sata ya fi daɗi; abincin da aka ci a ɓoye ya fi daɗi!”
18 And he has not known that Rephaim [are] there, Her invited ones in deep places of Sheol! (Sheol )
Amma ba su san cewa matattu suna a can ba, cewa baƙinta suna a can cikin zurfin kabari ba. (Sheol )