< Proverbs 31 >

1 Words of Lemuel, a king, a declaration that his mother taught him:
Maganganun Sarki Lemuwel, magana ce horarriya mahaifiyarsa ta koya masa,
2 “What, my son? And what, son of my womb? And what, son of my vows?
“Ka saurara, ya ɗana! Ka saurara, ɗan cikina! Ka saurara, ya ɗan amshin addu’ata!
3 Do not give your strength to women, And your ways to wiping away of kings.
Kada ka ba da ƙarfinka a kan mata, ƙarfinka ga waɗanda suka hallaka sarakuna.
4 [It is] not for kings, O Lemuel, Not for kings, to drink wine, And for princes—a desire of strong drink.
“Ba na sarakuna ba ne, ya Lemuwel, ba na sarakuna ba ne su sha ruwan inabi, ba na masu mulki ba ne su yi marmarin barasa,
5 Lest he drink, and forget the decree, And change the judgment of any of the sons of affliction.
don kada su sha su manta da abin da doka ta umarta, su hana wa waɗanda aka danne hakkinsu.
6 Give strong drink to the perishing, And wine to the bitter in soul,
A ba da barasa ga waɗanda suke cikin halin ƙaƙa naka yi, ruwan inabi ga waɗanda suke cikin wahala;
7 He drinks, and forgets his poverty, And he does not remember his misery again.
bari su sha su manta da talaucinsu kada kuma su ƙara tunawa da ɓacin ransu.
8 Open your mouth for the mute, For the right of all sons of change.
“Yi magana domin bebaye, domin hakkin dukan waɗanda suke naƙasassu.
9 Open your mouth, judge righteously, Both the cause of the poor and needy!”
Yi magana a kuma yi shari’ar adalci; a tsare hakkin talakawa da masu bukata.”
10 [ALEPH-BET] A woman of worth who finds? Indeed, her price [is] far above rubies.
Wa yake iya samun mace mai halin kirki? Darajarta ta fi ta lu’ulu’ai.
11 The heart of her husband has trusted in her, And he does not lack spoil.
Mijinta yana da cikakken amincewa da ita kuma ba ya rasa wani abu mai daraja.
12 She has done him good, and not evil, All [the] days of her life.
Takan yi masa alheri ba mugunta ba, dukan kwanakin ranta.
13 She has sought wool and flax, And with delight she works [with] her hands.
Takan zaɓi ulu da lilin ta yi ta saƙa da hannuwanta da farin ciki.
14 She has been as ships of the merchant, She brings in her bread from afar.
Ita kamar jirgin’yan kasuwa ne tana kawo abincinta daga nesa.
15 Indeed, she rises while yet night, And gives food to her household, And a portion to her girls.
Takan farka tun da sauran duhu; ta tanada wa iyalinta abinci ta kuma shirya wa’yan matan gidanta ayyukan da za su yi.
16 She has considered a field, and takes it, She has planted a vineyard from the fruit of her hands.
Takan lura da gona sosai ta kuma saye ta; daga abin da take samu na kuɗin shiga take shuka gonar inabi.
17 She has girded her loins with might, And strengthens her arms.
Takan himmantu tă yi aikinta tuƙuru; hannuwanta suna da ƙarfi domin ayyukanta.
18 She has perceived when her merchandise [is] good, Her lamp is not extinguished in the night.
Takan tabbata akwai riba a kasuwancinta, kuma fitilarta ba ya mutuwa da dare.
19 She has sent forth her hands on a spindle, And her hands have held a distaff.
Da hannunta take riƙe abin kaɗi ta kuma kama abin saƙa da yatsotsinta.
20 She has spread forth her hand to the poor, Indeed, she sent forth her hands to the needy.
Takan marabci talakawa takan kuma taimaki masu bukata.
21 She is not afraid of her household from snow, For all her household are clothed [with] scarlet.
Sa’ad da ƙanƙara ta fāɗi, ba ta jin tsoro saboda gidanta; gama dukansu suna da tufafi masu kauri.
22 She has made ornamental coverings for herself, Silk and purple [are] her clothing.
Takan yi wa gadonta kayan shimfiɗa; tufafinta kuma na lilin ne mai laushi na shunayya.
23 Her husband is known in the gates, In his sitting with [the] elderly of [the] land.
Ana girmama mijinta a ƙofar shiga birni inda yakan zauna a cikin dattawan gari.
24 She has made linen garments, and sells, And she has given a girdle to the merchant.
Takan yi riguna na lilin ta sayar; takan kuma sayar wa’yan kasuwa da ɗamara.
25 Strength and honor [are] her clothing, And she rejoices at a latter day.
Ƙarfi da mutunci su ne suturarta; za tă iya yin dariyar kwanaki masu zuwa.
26 She has opened her mouth in wisdom, And the law of kindness [is] on her tongue.
Tana magana da hikima, kuma umarnai mai aminci yana a harshenta.
27 She [is] watching the ways of her household, And she does not eat bread of sloth.
Tana lura da sha’anin gidanta kuma ba ta cin abincin ƙyuya.
28 Her sons have risen up, and pronounce her blessed, Her husband, and he praises her,
’Ya’yanta sukan tashi su ce da ita mai albarka; haka mijinta ma, yakan kuma yabe ta yana cewa,
29 “The daughters who have done worthily [are] many, You have gone up above them all.”
“Mata da yawa suna yin abubuwan yabo, amma ke kin fi su duka.”
30 Favor [is] deceitful, and beauty [is] vain, A woman fearing YHWH, she may boast herself.
Kayan tsari yana ruɗu, kyau kuma kan shuɗe; amma mace mai tsoron Ubangiji abar yabo ce.
31 Give to her of the fruit of her hands, And her works praise her in the gates!
Ka ba ta ladar da ya dace tă samo wa kanta, bari kuma ayyukanta su kawo mata yabo a ƙofar shiga birni.

< Proverbs 31 >