< Philippians 3 >
1 As to the rest, my brothers, rejoice in the LORD; indeed, [it] is not tiresome to me to write to you the same things, and for you [is] sure.
A ƙarshe,’yan’uwana, ku yi farin ciki a cikin Ubangiji! Ba abin damuwa ba ne a gare ni in sāke rubuta muku irin waɗannan abubuwa, domin lafiyarku ne.
2 Look out for the dogs! Look out for the evil-workers! Look out for the mutilation!
Ku yi hankali da waɗancan karnuka, waɗancan mutane masu aikata mugunta, waɗancan masu yankan jiki.
3 For we are the circumcision, who are serving God by the Spirit, and glorying in Christ Jesus, and having no trust in flesh,
Gama mu ne masu kaciya, mu da muke yi sujada ta wurin Ruhun Allah, mu da muke taƙama a cikin Kiristi Yesu, mu da ba mu dogara da ayyukan da ake gani ba,
4 though I also have [cause of] trust in flesh. If any other one thinks to have trust in flesh, I more:
ko da yake ni kaina ina da dalilan dogara da haka. In kuwa akwai wani wanda yake tsammani yana da dalilan dogara ga jiki, ni fa na fi shi,
5 circumcision on the eighth day! Of the race of Israel! Of the tribe of Benjamin! A Hebrew of Hebrews! According to law—a Pharisee!
an yi mini kaciya a rana ta takwas, asalina Isra’ila ne, na kabilar Benyamin, mutumin Ibraniyawa ɗan Ibraniyawa; bisa ga doka kuwa ni Bafarisiye ne;
6 According to zeal—persecuting the Assembly! According to righteousness that is in law—becoming blameless!
wajen himma kuwa, ni mai tsananta wa ikkilisiya ne, wajen aikin adalci bisa ga hanyar doka, ni marar laifi ne.
7 But what things were gains to me, these I have counted loss, because of the Christ;
Amma abin da dā ya zama mini riba yanzu, na ɗauka hasara ce saboda Kiristi.
8 yes, indeed, and I count all things to be loss, because of the excellence of the knowledge of Christ Jesus my Lord, because of whom I suffered loss of all things, and count them to be refuse, that I may gain Christ, and be found in Him,
Me kuma ya fi, na ɗauki dukan abubuwa hasara ne in aka kwatanta da mafificiyar girman sanin Kiristi Yesu Ubangijina, wanda saboda shi ne na yi hasarar kome. Na mai da su kayan wofi, domin in sami Kiristi
9 not having my righteousness, which [is] of law, but that which [is] through faith from Christ—the righteousness that is of God by faith,
a kuma same ni a cikinsa, ba da wani adalcin kaina wanda yake zuwa daga bin doka ba, sai dai adalcin da yake samuwa ta wurin bangaskiya a cikin Kiristi, adalcin da yake fitowa daga Allah da kuma yake zuwa ta wurin bangaskiya.
10 to know Him, and the power of His resurrection, and the fellowship of His sufferings, being conformed to His death,
Ina so in san Kiristi da ikon tashinsa daga matattu da kuma zumuncin tarayya cikin shan wahalarsa, in kuma zama kamar sa a cikin mutuwarsa,
11 if anyhow I may attain to the resurrection of the dead.
yadda kuma ko ta yaya, in kai ga tashin nan daga matattu.
12 Not that I already obtained, or have already been perfected, but I pursue, if I also may lay hold of that for which I was also laid hold of by Christ Jesus;
Ba cewa na riga na sami dukan wannan ba ne, ko kuma an riga an mai da ni cikakke ba, sai dai ina nacewa don in kai ga samun abin da Kiristi Yesu ya riƙe ni saboda shi.
13 brothers, I do not reckon myself to have laid hold [of it], but one thing [I do]—indeed forgetting the things behind, and stretching forth to the things before—
’Yan’uwa, ban ɗauki kaina a kan cewa na riga na sami abin ba. Sai dai abu guda nake yi. Ina mantawa da abin da yake baya, ina kuma nacewa zuwa ga samun abin da yake gaba,
14 I pursue to the mark for the prize of the high calling of God in Christ Jesus.
ina nacewa gaba zuwa ga manufar, don in sami ladar da Allah ya yi mini na kiran nan zuwa sama a cikin Kiristi Yesu.
15 As many, therefore, as [are] perfect—let us think this, and if [in] anything you think otherwise, this also will God reveal to you,
Dukanmu da muka balaga ya kamata mu yi wannan irin ganin abubuwa. In kuwa saboda wani dalili tunaninku ya yi dabam, Allah zai bayyana muku wannan ma.
16 but to what we have attained—walk by the same rule, think the same thing;
Sai dai a duk inda muka kai, mu ci gaba da haka.
17 together become my followers, brothers, and observe those thus walking, according as you have us—a pattern;
Ku haɗa kai da waɗansu cikin bin gurbina, ku kuma lura da waɗanda suke rayuwa bisa ga ƙa’idar da muka ba ku.
18 for many walk of whom I told you [about] many times—and now also weeping tell—[they are] the enemies of the Cross of the Christ,
Gama kamar yadda na sha gaya muku yanzu kuma ina sāke gaya muku har ma da hawaye, waɗansu da yawa suna rayuwa kamar abokan gāban gicciyen Kiristi.
19 whose end [is] destruction, whose god [is] the belly, and whose glory [is] in their shame, who are minding the things on earth.
Ƙaddararsu hallaka ce, allahnsu cikinsu ne, rashin kunyarsu shi ne abin fahariyarsu. Hankalinsu yana kan kayan duniya.
20 For our citizenship is in the heavens, from where we also await a Savior—the Lord Jesus Christ—
Amma mu’yan mulkin sama ne. Muna kuma jira zuwan Mai Ceto daga can, Ubangiji Yesu Kiristi,
21 who will transform the body of our humiliation to its becoming conformed to the body of His glory, according to the working of His power, even to subject all things to Himself.
shi ne mai ikon kawo dukan abubuwa ƙarƙashin mulkinsa. Ta wurin ikon nan nasa zai sāke jikin nan namu na ƙasƙanci, yă mai da shi kamar jikin nan nasa na ɗaukaka.