< Numbers 13 >
1 And YHWH speaks to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “Send men for yourself, and they spy out the land of Canaan, which I am giving to the sons of Israel; one man—you send one man for the tribe of his fathers, everyone a prince among them.”
“Ka aiki waɗansu mutane zuwa ƙasar Kan’ana, wadda nake ba Isra’ilawa. Daga kowace kabila, ka aiki ɗaya daga cikin shugabanninta.”
3 And Moses sends them from the wilderness of Paran by the command of YHWH; all of them [are] men, [and] they are heads of the sons of Israel,
Saboda haka bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya aike su daga Hamadan Faran. Dukansu kuwa shugabanni ne na Isra’ilawa.
4 and these [are] their names: for the tribe of Reuben, Shammua son of Zaccur;
Shugabannin kuwa su ne, Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ruben;
5 for the tribe of Simeon, Shaphat son of Hori;
Shafat ɗan Hori, daga kabilar Simeyon;
6 for the tribe of Judah, Caleb son of Jephunneh;
Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
7 for the tribe of Issachar, Igal son of Joseph;
Igal ɗan Yusuf, daga kabilar Issakar;
8 for the tribe of Ephraim, Oshea son of Nun;
Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Efraim;
9 for the tribe of Benjamin, Palti son of Raphu;
daga kabilar Benyamin, Falti ɗan Rafu;
10 for the tribe of Zebulun, Gaddiel son of Sodi;
Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zebulun;
11 for the tribe of Joseph (for the tribe of Manasseh), Gaddi son of Susi;
Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manasse (wata kabilar Yusuf);
12 for the tribe of Dan, Ammiel son of Gemalli;
Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan;
13 for the tribe of Asher, Sethur son of Michael;
Setur ɗan Mika’ilu, daga kabilar Asher;
14 for the tribe of Naphtali, Nahbi son of Vopshi;
Nabi ɗan Bofsi, daga kabilar Naftali;
15 for the tribe of Gad, Geuel son of Machi.
Geyuwel ɗan Maki, daga kabilar Gad.
16 These [are] the names of the men whom Moses has sent to spy out the land; and Moses calls Hoshea son of Nun, Joshua.
Waɗannan su ne sunayen mutanen da Musa ya aika su binciki ƙasar. (Sai Musa ya ba Hosheya ɗan Nun, suna Yoshuwa.)
17 And Moses sends them to spy out the land of Canaan and says to them, “Go up this [way] into the south, and you have gone up the mountain,
Sa’ad da Musa ya aike su domin su binciki Kan’ana ya ce, “Ku haura, ku ratsa ta Negeb har zuwa ƙasar tudu.
18 and have seen the land, what it [is], and the people which is dwelling on it, whether it [is] strong or feeble, [and] whether it [is] few or many;
Ku ga yadda ƙasar take, ku ga ko mutanen da suke zama a can ƙarfafa ne, ko raunannu, ko su kima ne, ko kuma suna da yawa.
19 and what the land [is] in which it is dwelling, whether it [is] good or bad; and what [are] the cities in which it is dwelling, whether in camps or in fortresses.
Wace irin ƙasa ce suke zama a ciki, Mai kyau ce, ko mummuna? Waɗanne irin birane ne suke zama a ciki? Suna da katanga, ko babu?
20 And what the land [is], whether it [is] fat or lean; whether there is wood in it or not; and you have strengthened yourselves, and have taken of the fruit of the land”; now the days [are] days of the first-fruits of grapes.
Yaya ƙasar take? Tana da wadata, ko babu? Akwai itatuwa, ko babu? Ku yi iya ƙoƙarinku ku ɗebo daga cikin albarkar ƙasar ku kawo.” (Lokacin farkon nunan inabi ne.)
21 And they go up and spy out the land, from the wilderness of Zin to Rehob at the going in to Hamath;
Saboda haka suka haura, suka binciki ƙasar daga Hamadan Zin har zuwa Rehob, wajen Lebo Hamat.
22 and they go up by the south, and come to Hebron, and there [are] Ahiman, Sheshai, and Talmai, children of Anak (and Hebron was built seven years before Zoan in Egypt),
Suka kuma haura ta Negeb, suka iso Hebron, inda Ahiman, da Sheshai, da Talmai, zuriyar Anak, suke zama. (An gina Hebron da shekara bakwai kafin a gina Zowan a Masar.)
23 and they come to the Brook of Eshcol, and cut down a branch and one cluster of grapes there, and they carry it on a staff by two, also [some] of the pomegranates, and of the figs.
Da suka iso Kwarin Eshkol, sai suka yanko reshe guda na nonon inabi tare da’ya’yansa cunkus. Mutum biyu suka ɗauka shi rataye a sanda a kafaɗarsu, suka haɗa tare da rumman da kuma ɓaure.
24 That place has been called the Brook of Eshcol, because of the cluster which the sons of Israel cut from there.
Sai aka kira wurin Kwarin Eshkol saboda nonon inabin da suka yi cunkus, wanda Isra’ilawa suka yanko a wurin.
25 And they return from spying out the land at the end of forty days.
A ƙarshen kwana arba’in sai suka komo daga bincikensu.
26 And they go and come to Moses, and to Aaron, and to all the congregation of the sons of Israel, to the wilderness of Paran, to Kadesh; and they bring them and all the congregation back word, and show them the fruit of the land.
Suka dawo wurin Musa, da Haruna, da dukan jama’ar Isra’ilawa, a Kadesh, a Hamadan Faran. A can suka ba da rahoton ga dukan taron da yake wurin, suka kuma nuna musu amfanin ƙasar.
27 And they recount to him, and say, “We came to the land to where you have sent us, and it is indeed flowing with milk and honey—and this [is] its fruit;
Suka ce wa Musa, “Mun je ƙasar da ka aike mu, ƙasar tana zub da madara da zuma! Ga kuma amfaninta.
28 only, surely the people which is dwelling in the land [is] strong; and the cities are fortified [and] very great; and we have also seen children of Anak there.
Amma fa mazaunan can ɗin ƙarfafa ne, an kuma kewaye biranen da manya-manyan katanga. Mun kuma ga zuriyar Anak a can.
29 Amalek is dwelling in the land of the south, and the Hittite, and the Jebusite, and the Amorite are dwelling in the hill country, and the Canaanite is dwelling by the sea, and by the side of the Jordan.”
Amalekawa suna zama a Negeb; Hittiyawa, Yebusiyawa da kuma Amoriyawa, suna zama ne a ƙasar tudu. Kan’aniyawa kuma suna zama kusa da teku da kuma a bakin Urdun.”
30 And Caleb stills the people concerning Moses and says, “Let us certainly go up—and we have possessed it; for we are thoroughly able to [do] it.”
Sai Kaleb ya sa mutane suka yi shiru a gaban Musa, sai ya ce, “Ya kamata mu tafi mu mallaki ƙasar, gama lalle za mu iya cinta.”
31 And the men who have gone up with him said, “We are not able to go up against the people, for it [is] stronger than we”;
Amma sauran mutanen da suka je tare da shi, suka ce, “Ba za mu iya kara da mutanen nan ba; sun fi mu ƙarfi.”
32 and they bring out an evil account of the land which they have spied out to the sons of Israel, saying, “The land into which we passed over to spy it out is a land eating up its inhabitants; and all the people whom we saw in its midst [are] men of stature;
Sai suka yaɗa labari marar kyau ga Isra’ilawa game da ƙasar da suka binciko. Suka ce, “Ƙasar da muka ratsa cikinta domin mu leƙi asirinta, tana cinye waɗanda suke zama a cikinta. Dukan mutanen da muka gani a wurin, ƙatti ne.
33 and there we saw the giants, sons of Anak, of the giants; and we are as grasshoppers in our own eyes—and so we were in their eyes.”
Mun ga Nefilimawa a can (zuriyar Anak sun fito ne daga Nefilim). Sai muka ga kanmu kamar fāra ne kawai, haka kuwa muke a gare su.”