< Numbers 11 >

1 And the people are evil, as those sighing habitually in the ears of YHWH, and YHWH hears, and His anger burns, and the fire of YHWH burns among them, and consumes in the extremity of the camp.
Da Ubangiji ya ji gunagunin da mutanen suke yi saboda wahalarsu, sai ya husata ƙwarai. Sai wuta daga Ubangiji ta yi ta ci a cikinsu har ta ƙone waɗansu wurare na sansanin.
2 And the people cry to Moses, and Moses prays to YHWH, and the fire is quenched;
Da jama’ar suka yi wa Musa kuka, sai ya yi addu’a ga Ubangiji, wutar kuwa ta mutu.
3 and he calls the name of that place Taberah, for the fire of YHWH has “burned” among them.
Saboda haka aka kira wannan wuri Tabera, gama a wurin ne wuta daga Ubangiji ta ƙuna a cikinsu.
4 And the rabble who [are] in its midst have lusted greatly, and the sons of Israel also turn back and weep, and say, “Who gives us flesh?
Wata rana, baƙin da suke cikinsu, suka fara kwaɗayin waɗansu abinci, har suka sa Isra’ilawa suka fara kuka, suna cewa, “Da mun sami nama mun ci mana!
5 We have remembered the fish which we eat in Egypt for nothing, the cucumbers, and the melons, and the leeks, and the onions, and the garlic;
Mun tuna da kifin da muka ci kyauta a Masar, haka ma kayan lambu irin su kukumba, guna, safa, albasa da kuma tafarnuwa.
6 and now our soul [is] dry, there is not anything, except the manna, before our eyes.”
Amma ga shi yanzu ba mu da wani abin marmari; in ba wannan Manna ba!”
7 And the manna is as coriander seed, and its aspect as the aspect of bdellium;
Manna kuwa kamar tsabar riɗi take, kamanninta kuma kamar ƙaro ne.
8 the people have turned aside and gathered [it], and ground [it] with millstones, or beat [it] in a mortar, and boiled [it] in a pan, and made it cakes, and its taste has been as the taste of the moisture of oil.
Mutane sukan fita su tattara ta, su niƙa a dutsen niƙa, ko kuwa su daka a turmi. Su dafa, ko su yi waina da ita. Ɗanɗanonta yakan yi kamar abin da aka yi da man zaitun.
9 And in the descending of the dew on the camp by night, the manna descends on it.
Sa’ad da raɓa tana saukowa da dad dare a kan sansani, Manna ma takan sauko.
10 And Moses hears the people weeping by its families, each at the opening of his tent, and the anger of YHWH burns exceedingly, and in the eyes of Moses [it is] evil.
Musa ya ji mutanen suna ta gunaguni ko’ina a cikin iyalansu, kowane mutum a ƙofar tentinsa. Ubangiji kuwa ya husata ƙwarai, sai Musa ya damu.
11 And Moses says to YHWH, “Why have You done evil to Your servant? And why have I not found grace in Your eyes—to put the burden of all this people on me?
Sai ya ce wa Ubangiji, “Me ya sa ka kawo wannan damuwar a kan bawanka? Me na yi da ya ɓata maka rai har ka ɗora dukan nauyin mutanen nan a kaina?
12 I—have I conceived all this people? I—have I begotten it, that You say to me, Carry it in your bosom, as the one supporting carries the nursing suckling, to the ground which You have sworn to its fathers?
Ni ne na yi cikin dukan mutanen nan? Ni ne na haife su? To, me ya sa ka ce in ɗauke su a ƙirjina kamar yadda mai reno yake rungume jariri, zuwa ƙasa wadda ka yi alkawari da rantsuwa za ka ba wa kakanninsu?
13 From where do I have flesh to give to all this people? For they weep to me, saying, Give flesh to us, and we eat.
Ina ne zan sami nama in waɗannan mutane? Sun dinga yin mini kuka suna cewa ‘Ka ba mu nama mu ci!’
14 I am not able—I alone—to bear all this people, for [it is] too heavy for me;
Ba zan iya ɗaukan dukan mutanen nan ni kaɗai ba, nauyin ya yi mini yawa.
15 and if thus You are doing to me—please slay me; slay, if I have found grace in your eyes, and do not let me look on my affliction.”
In haka za ka yi da ni, ka kashe ni yanzu, in na sami tagomashi daga gare ka, kada ka bar ni in rayu in ga wannan baƙin ciki.”
16 And YHWH says to Moses, “Gather to Me seventy men from [the] elderly of Israel, whom you have known that they are [the] elderly of the people, and its authorities; and you have taken them to the Tent of Meeting, and they have stationed themselves there with you,
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tattaro mini dattawa saba’in daga cikin mutanen Isra’ila, waɗanda aka sani su ne dattawa da kuma shugabanni a cikin jama’a. Ka sa su zo Tentin Sujada, su tsaya a can tare da kai.
17 and I have come down and spoken with you there, and have kept back of the Spirit which [is] on you, and have put [that One] on them, and they have borne some of the burden of the people with you, and you do not bear [it] alone.
Zan sauko in yi magana da kai a can, zan kuma ɗauki Ruhun da yake kanka in mai da shi wajensu. Za su taimake ka ɗaukan nauyin mutane, don yă zama ba kai kaɗai ba ne mai ɗaukan kaya.
18 And you say to the people: Sanctify yourselves for tomorrow, and you have eaten flesh, for you have wept in the ears of YHWH, saying, Who gives us flesh? For we [had] good in Egypt; and YHWH has given flesh to you, and you have eaten.
“Ka gaya wa mutane, ‘Ku tsarkake kanku don gobe, za ku ci nama. Ubangiji ya ji ku sa’ad da kuka yi kuka cewa, “Da mun sami nama mun ci mana! Ai, da ba mu da damuwa, gama lokacin da muke zama cikin Masar ba mu da damuwa!” Yanzu Ubangiji zai ba ku nama, za ku kuma ci.
19 You do not eat one day, nor two days, nor five days, nor ten days, nor twenty days,
Ba za ku ci shi na kwana ɗaya, ko biyu, ko biyar, ko goma, ko kuma kwana ashirin kaɗai ba,
20 [but] even to a month of days, until it comes out from your nostrils, and it has become an abomination to you, because that you have loathed YHWH, who [is] in your midst, and weep before Him, saying, Why is this [that] we have come out of Egypt!”
amma za ku ci har na wata guda cur, sai ya gundure ku a hanci har ku yi ƙyamarsa, domin kun ƙi Ubangiji wanda yake cikinku, kuka yi kuka a gabansa, kuna cewa, “Don me ma muka bar ƙasar Masar?”’”
21 And Moses says, “Six hundred thousand footmen [are] the people in whose midst I [dwell]; and You, You have said, I give flesh to them, and they have eaten [for] a month of days!
Amma Musa ya ce, “Ga ni a cikin mutane dubu ɗari shida tafe tare da ni, kana kuma cewa, ‘Zan ba su nama su ci har wata guda cur!’
22 Is flock and herd slaughtered for them, that one has found [enough] for them? Are all the fishes of the sea gathered for them, that one has found [enough] for them?”
Za su ma sami isashe in har aka yanka musu garkuna tumaki da na shanu? Za su sami isashe in aka kama musu dukan kifin teku?”
23 And YHWH says to Moses, “Has the hand of YHWH become short? Now you see whether My word meets you or not.”
Ubangiji ya ce wa Musa, “Akwai abin da ya fi ƙarfina ne? Bari ka gani ko abin da na ce zan yi, zai faru ko babu.”
24 And Moses goes out, and speaks the words of YHWH to the people, and gathers seventy men from [the] elderly of the people, and causes them to stand around the tent,
Saboda haka Musa ya fita ya gaya wa jama’a abin da Ubangiji ya faɗa. Ya tattaro dattawansu saba’in, ya sa suka tsaya kewaye da Tentin Sujada.
25 and YHWH comes down in the cloud, and speaks to him, and keeps back of the Spirit which [is] on him, and puts [that One] on the seventy elderly men; and it comes to pass at the resting of the Spirit on them, that they prophesy, and they have never done [so] again.
Sa’an nan Ubangiji ya sauko daga girgije, ya yi magana da shi, ya kuma ɗauke Ruhun da yake kan Musa ya ɗora shi a kan dattawa saba’in nan. Sa’ad da Ruhun ya zauna a kansu, sai suka yi annabci, amma daga wannan ba su ƙara yin haka kuma ba.
26 And two of the men are left in the camp, the name of the first [is] Eldad and the name of the second Medad, and the spirit rests on them (and they are among those written, but they have not gone out to the tent), and they prophesy in the camp;
To, fa, akwai dattawa biyu da suka kasance a sansani, wato, Eldad da Medad. Su ma an lasafta su cikin dattawan, amma ba su fita zuwa Tentin Sujada ba. Duk da haka Ruhun ya sauka a kansu, suka kuma yi annabci a cikin sansanin.
27 and the young man runs, and declares [it] to Moses, and says, “Eldad and Medad are prophesying in the camp.”
Wani saurayi ya sheƙa a guje zuwa wajen Musa ya ce, “Eldad da Medad suna can suna annabci a sansani.”
28 And Joshua son of Nun, minister of Moses, [one] of his young men, answers and says, “My lord Moses, restrain them.”
Sai Yoshuwa ɗan Nun, wanda yake mataimakin Musa tun yana saurayi, ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, Musa, ka hana su!”
29 And Moses says to him, “Are you zealous for me? O that all YHWH’s people were prophets! That YHWH would put His Spirit on them!”
Amma Musa ya amsa ya ce, “Kana kishi domina ne? Da ma a ce dukan mutanen Ubangiji annabawa ne, da ma a kuma ce Ubangiji ya sa Ruhunsa a kansu mana!”
30 And Moses is gathered to the camp, he and [the] elderly of Israel.
Sai Musa da dattawan Isra’ila suka koma sansani.
31 And a spirit has journeyed from YHWH, and cuts off quails from the sea, and leaves [them] by the camp, as a day’s journey here and as a day’s journey there, around the camp, and about two cubits above the face of the land.
Ana nan, sai Ubangiji ya kawo wata iska mai tsanani ta koro makware daga teku. Ta bar su birjik kewaye da sansani, tsayinsu daga ƙasa ya kai kamu biyu, misalin tafiyar nisan yini guda ta kowace fuska.
32 And the people rise all that day, and all the night, and all the day after, and gather the quails—he who has least has gathered ten homers—and they spread them out for themselves around the camp.
Dukan yini da dukan dare da kuma kashegari, mutane suka fito suka tattara makware. Ba wanda ya kāsa tara ƙasa da garwa goma. Sai suka shanya abinsu kewaye da sansanin.
33 The flesh is yet between their teeth—it is not yet cut off—and the anger of YHWH has burned among the people, and YHWH strikes [with] a very great striking among the people;
Amma da suna cikin cin naman, tun ba su ma haɗiye ba, sai Ubangiji ya husata sosai a kan jama’ar, ya buge su da annoba mai zafi.
34 and [one] calls the name of that place Kibroth-Hattaavah, for there they have buried the people who lust.
Saboda haka aka kira wannan wuri Kibrot Hatta’awa, gama a can ne aka binne mutanen nan makwaɗaita.
35 From Kibroth-Hattaavah the people have journeyed to Hazeroth, and they are in Hazeroth.
Daga Kibrot Hatta’awa, mutane suka yi tafiya zuwa Hazerot, a can suka sauka.

< Numbers 11 >