< Micah 6 >
1 Now hear that which YHWH is saying: “Rise—strive with the mountains, And cause the hills to hear your voice.
Ku saurari abin da Ubangiji ya ce, “Tashi ku gabatar da ƙararku a gaban duwatsu; bari tuddai su ji abin da kuke so ku faɗa.
2 Hear, O mountains, the strife of YHWH, You strong ones—foundations of earth! For a strife [is] to YHWH, with His people, And with Israel He reasons.
“Ku saurara, ya ku duwatsu game da tuhumar da Ubangiji yake muku, ku ji, ku daɗaɗɗun tushin duniya. Gama Ubangiji yana da ƙara a kan mutanensa; yana tuhumar Isra’ila.
3 O My people, what have I done to you? And how have I wearied you? Testify against Me.
“Ya ku mutanena, me na yi muku? Ta yaya na nawaita muku? Ku amsa mini.
4 For I brought you up from the land of Egypt, And I have ransomed you from the house of servants, And I send Moses, Aaron, and Miriam before you.
Na fito da ku daga ƙasar Masar na kuma’yantar da ku daga ƙasar bauta. Na aika da Musa yă jagorance ku, haka ma Haruna da Miriyam.
5 O My people, please remember What Balak king of Moab counseled, What Balaam son of Beor answered him (From Shittim to Gilgal), In order to know the righteous acts of YHWH.”
Ya ku mutanena, ku tuna abin da Balak sarkin Mowab ya ƙulla da kuma amsar da Bala’am ɗan Beyor ya bayar. Ku tuna da tafiyarku daga Shittim zuwa Gilgal, don ku san ayyukan adalcin Ubangiji.”
6 With what do I come before YHWH? Do I bow to God Most High? Do I come before Him with burnt-offerings? With calves—sons of a year?
Da me zan zo a gaban Ubangiji in rusuna a gaban Maɗaukaki Allah? Shin, zan zo ne a gabansa da hadaya ta ƙonawa, da ɗan maraƙi bana ɗaya?
7 Is YHWH pleased with thousands of rams? With myriads of streams of oil? Do I give my firstborn [for] my transgression? The fruit of my body [for] the sin of my soul?
Ubangiji zai ji daɗin hadayar raguna dubbai da kuma rafuffukan mai dubbai goma? Zan ba da ɗan farina ne don laifina, ko’ya’yan jikina domin zunubin raina?
8 He has declared to you, O man, what [is] good; Indeed, what is YHWH requiring of you, Except—to do judgment, and love kindness, And to walk lowly with your God?
Ya nuna maka, ya mutum, abin da yake mai kyau. Me Ubangiji yake bukata daga gare ka kuwa shi ne ka yi gaskiya ka so aikata jinƙai ka kuma yi tafiya da tawali’u a gaban Allah.
9 A voice of YHWH calls to the city, And wisdom fears Your Name, “Hear the rod, and Him who appointed it.
Ku saurara! Ubangiji yana kira ga birni, a ji tsoron sunana kuwa hikima ce, “Ku kasa kunne ga sandan nan da kuma wannan wanda ya naɗa.
10 Are there yet [in] the house of the wicked Treasures of wickedness, And the abhorred meager ephah?
Har yanzu zan manta, ya muguwar gida da dukiyarki da kika samu a muguwar hanya zan kuma manta da bugaggen mudun awo wanda ake zargi?
11 Do I reckon [it] pure with balances of wickedness? And with a bag of deceitful stones?
Zan kuɓutar da mutumin da yake da ma’auni na rashin gaskiya, da kuma buhun ma’aunan ƙarya?
12 Whose rich ones have been full of violence, And its inhabitants have spoken falsehood, And their tongue [is] deceitful in their mouth.
Attajiranta masu fitina ne; mutanenta kuma maƙaryata ne harsunansu kuwa suna yaudara.
13 And I also, I have begun to strike you, To make desolate, because of your sins.
Saboda haka, zan hallaka ku in lalace ku saboda zunubanku.
14 You eat, and you are not satisfied, And your pit [is] in your midst, And you remove, and do not deliver, And that which you deliver, I give to a sword.
Za ku ci amma ba za ku ƙoshi ba, cikinku zai zama babu kome Za ku tattara amma ba za ku yi ajiyar kome ba, gama abin da kuka yi ajiya zan ba wa takobi.
15 You sow, and you do not reap, You tread the olive, And you do not pour out oil, And new wine—and you do not drink wine.
Za ku yi shuki amma ba za ku girba ba; za ku matse zaitun amma ba za ku yi amfani da mai wa kanku ba, za ku tattaka’ya’yan inabi amma ba za ku sha ruwan inabin ba.
16 And the statutes of Omri are kept habitually, And all the work of the house of Ahab, And you walk in their counsels, For My giving you for a desolation, And its inhabitants for a hissing, And you bear the reproach of My people!”
Kuna kiyaye ƙa’idodin Omri da dukan ayyukan gidan Ahab kun kuma bi al’adunsu. Saboda haka, zan maishe ku kufai in mai da ku abin dariya a cikin mutane, za ku sha reni a wurin al’ummai.”