< Matthew 8 >
1 And when He came down from the mountain, great multitudes followed Him,
Da ya sauko daga dutsen, sai taron mutane mai yawan gaske suka bi shi.
2 and behold, a leper having come, was prostrating to Him, saying, “Lord, if You are willing, You are able to cleanse me”;
Wani mutum mai kuturta ya zo ya durƙusa a gabansa ya ce, “Ubangiji, in kana so, kana iya tsabtacce ni.”
3 and having stretched forth the hand, Jesus touched him, saying, “I will, be cleansed,” and immediately his leprosy was cleansed.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin. Ya ce, “Ina so, ka tsabtacce!” Nan da nan aka warkar da shi daga kuturtarsa.
4 And Jesus says to him, “See, you may tell no one, but go, show yourself to the priest, and bring the gift that Moses commanded for a testimony to them.”
Sai Yesu ya ce masa, “Ka lura kada ka gaya wa kowa. Sai dai ka tafi, ka nuna kanka ga firist ka kuma yi bayarwar da Musa ya umarta, a matsayin shaida gare su.”
5 And Jesus having entered into Capernaum, there came to Him a centurion calling on Him,
Da Yesu ya shiga Kafarnahum, sai wani jarumi ya zo wurinsa, yana neman taimako.
6 and saying, “Lord, my young man has been laid in the house a paralytic, fearfully afflicted,”
Ya ce, “Ubangiji, bawana yana kwance a gida shanyayye, yana kuma shan azaba ƙwarai.”
7 and Jesus says to him, “I, having come, will heal him.”
Yesu ya ce masa, “Zan je in warkar da shi.”
8 And the centurion answering said, “Lord, I am not worthy that You may enter under my roof, but only say a word, and my servant will be healed;
Jarumin ya amsa, “Ubangiji, ban cancanci in sa ka zo gidana ba, ka dai yi magana kawai, bawana zai warke.
9 for I also am a man under authority, having under myself soldiers, and I say to this one, Go, and he goes, and to another, Be coming, and he comes, and to my servant, Do this, and he does [it].”
Gama ni kaina mutum ne a ƙarƙashin iko, da kuma sojoji a ƙarƙashina. Nakan ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai yă tafi; wancan kuma, ‘Zo nan,’ sai yă zo. Nakan ce wa bawana, ‘Yi wannan,’ sai kuwa yă yi.”
10 And Jesus having heard, wondered, and said to those following, “Truly I say to you, not even in Israel have I found such great faith;
Da Yesu ya ji wannan, sai ya yi mamaki ya kuma ce wa waɗanda suke binsa, “Gaskiya nake gaya muku, ban taɓa samun wani a Isra’ila da bangaskiya mai girma haka ba.
11 and I say to you that many from east and west will come and recline with Abraham, and Isaac, and Jacob, in the kingdom of the heavens,
Ina kuma gaya muku da yawa za su zo daga gabas da kuma yamma, su ɗauki wuraren zamansu a biki tare da Ibrahim, Ishaku, da Yaƙub a cikin mulkin sama.
12 but the sons of the kingdom will be cast forth into the outer darkness—there will be the weeping and the gnashing of the teeth.”
Amma za a jefar da’ya’yan mulki waje, zuwa cikin baƙin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.”
13 And Jesus said to the centurion, “Go, and as you believed let it be to you”; and his young man was healed in that hour.
Sa’an nan Yesu ya ce wa jarumin, “Je ka! Za a yi bisa ga bangaskiyarka.” A daidai wannan lokaci bawansa kuwa ya warke.
14 And Jesus having come into the house of Peter, saw his mother-in-law laid, and fevered,
Da Yesu ya zo cikin gidan Bitrus, sai ya ga surukar Bitrus tana kwance a gado tana da zazzaɓi.
15 and He touched her hand, and the fever left her, and she arose, and was ministering to them.
Ya taɓa hannunta sai zazzaɓin ya sake ta, ta kuwa tashi ta fara yin masa hidima.
16 And evening having come, they brought to Him many demoniacs, and He cast out the spirits with a word, and healed all who were ill,
Da yamma ta yi, aka kawo masa masu aljanu da yawa, ya kuwa fitar da ruhohin ta wurin magana, ya kuma warkar da dukan marasa lafiya.
17 that it might be fulfilled that was spoken through Isaiah the prophet, saying, “He took our sicknesses Himself, and bore the diseases.”
Wannan ya faru ne domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya cewa, “Ya ɗebi rashin lafiyarmu, ya kuma ɗauki cututtukanmu.”
18 And Jesus having seen great multitudes around Him, commanded to depart to the other side;
Da Yesu ya ga taron mutane kewaye da shi, sai ya ba da umarni a ƙetare zuwa ɗayan hayin tafkin.
19 and a certain scribe having come, said to Him, “Teacher, I will follow You wherever You may go”;
Sai wani malamin dokoki ya zo wurinsa ya ce, “Malam, zan bi ka duk inda za ka.”
20 and Jesus says to him, “The foxes have holes, and the birds of the sky places of rest, but the Son of Man has nowhere He may lay the head.”
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Yanyawa suna da ramummuka, tsuntsayen sararin sama suna da sheƙuna, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin da zai sa kansa.”
21 And another of His disciples said to Him, “Lord, permit me first to depart and to bury my father”;
Sai wani almajiri ya ce masa, “Ubangiji, da farko bari in je in binne mahaifina.”
22 and Jesus said to him, “Follow Me, and permit the dead to bury their own dead.”
Amma Yesu ya ce masa, “Ka bi ni, ka bar matattu su binne matattunsu.”
23 And when He entered into the boat His disciples followed Him,
Sai ya shiga jirgin ruwa, almajiransa kuwa suka bi shi.
24 and behold, a great storm arose in the sea, so that the boat was being covered by the waves, but He was sleeping,
Ba zato ba tsammani, sai wani babban hadari ya taso a tafkin, har raƙuman ruwan suka sha kan jirgin. Amma Yesu yana barci.
25 and His disciples having come to Him, awoke Him, saying, “Lord, save us! We are perishing!”
Almajiran suka je suka tashe shi, suna cewa, “Ubangiji, ka cece mu! Za mu nutse!”
26 And He says to them, “Why are you fearful, O you of little faith?” Then having risen, He rebuked the winds and the sea, and there was a great calm;
Ya amsa ya ce, “Ku masu ƙarancin bangaskiya, me ya sa kuke tsoro haka?” Sa’an nan ya tashi ya tsawata wa iskar da kuma raƙuman ruwan, sai wuri ya yi tsit gaba ɗaya.
27 and the men wondered, saying, “What kind—is this, that even the wind and the sea obey Him?”
Mutanen suka yi mamaki suka ce, “Wane irin mutum ne wannan? Har iska da raƙuman ruwa suna masa biyayya!”
28 And He having come to the other side, to the region of the Gergesenes, there met Him two demoniacs, coming forth out of the tombs, very fierce, so that no one was able to pass over by that way,
Da ya isa ɗayan gefen a yankin Gadarenawa (ko kuwa Gerasenawa), sai ga mutum biyu masu aljanu suna fitowa daga kaburbura suka tarye shi. Su abin tsoro ne ƙwarai, har ba mai iya bin wannan hanya.
29 and behold, they cried out, saying, “What [regards] us and You, [[Jesus, ]] Son of God? Did You come here to afflict us before the time?”
Suka yi ihu suka ce, “Me ya haɗa ka da mu, Ɗan Allah?” Ka zo ne nan don ka ji mana kafin lokaci yă yi?
30 And there was a herd of many pigs feeding far off from them,
Nesa kaɗan da su kuwa akwai babban garken aladu da yake kiwo.
31 and the demons were calling on Him, saying, “If You cast us forth, permit us to go away into the herd of the pigs”;
Aljanun suka roƙi Yesu suka ce, “In ka fitar da mu, tura mu cikin garken aladun nan.”
32 and He says to them, “Go.” And having come forth, they went into the herd of the pigs, and behold, the whole herd of the pigs rushed down the steep, into the sea, and died in the waters,
Ya ce musu, “Ku tafi!” Sai suka fita suka shiga cikin aladun, dukan garken kuwa ya gangara a guje daga kan tudun zuwa cikin tafkin aladun kuma suka mutu a cikin ruwa.
33 and those feeding fled, and having gone into the city, they declared all, and the matter of the demoniacs.
Masu kiwon aladun suka ruga, suka je cikin gari suka ba da labarin dukan wannan, haɗe da abin da ya faru da mutanen nan masu aljanu.
34 And behold, all the city came forth to meet Jesus, and having seen Him, they called on [Him] that He might depart from their borders.
Sai dukan garin suka fito don su taryi Yesu. Da suka kuwa gan shi, sai suka roƙe shi yă bar musu yanki.