< Matthew 5 >
1 And having seen the multitudes, He went up to the mountain, and He having sat down, His disciples came to Him,
Da Yesu ya ga taron jama'ar, sai ya hau saman dutse. Sa'adda ya zauna, almajiransa suka zo wurinsa.
2 and having opened His mouth, He was teaching them, saying,
Ya bude bakinsa kuma ya koyar da su, yana cewa,
3 “Blessed the poor in spirit—because theirs is the kingdom of the heavens.
“Albarka ta tabbata ga masu talauci a ruhu, domin mulkin sama nasu ne.
4 Blessed the mourning—because they will be comforted.
Albarka ta tabbata ga masu makoki, domin za a ta'azantar da su.
5 Blessed the meek—because they will inherit the land.
Albarka ta tabbata ga masu tawali'u, domin za su gaji duniya.
6 Blessed those hungering and thirsting for righteousness—because they will be filled.
Albarka ta tabbata ga masu yunwa da kishin adalci, domin za a kosar da su.
7 Blessed the kind—because they will find kindness.
Albarka ta tabbata ga masu jinkai, domin za su samu jinkai.
8 Blessed the clean in heart—because they will see God.
Albarka ta tabbata ga masu tsabtar zuciya, domin za su ga Allah.
9 Blessed the peacemakers—because they will be called sons of God.
Albarka ta tabbata ga masu kawo salama, domin za a ce da su 'ya'yan Allah.
10 Blessed those persecuted for righteousness’ sake—because theirs is the kingdom of the heavens.
Albarka ta tabbata ga wadanda ake tsananta masu saboda adalci, domin mulkin sama nasu ne.
11 Blessed are you whenever they may reproach you, and may persecute, and may say any evil thing against you falsely for My sake—
Masu albarka ne ku sa'adda mutane suka zage ku, suka kuma tsananta maku, ko kuwa suka zarge ku da dukan miyagun abubuwa iri iri na karya, saboda ni.
12 rejoice and be glad, because your reward [is] great in the heavens, for thus they persecuted the prophets who were before you.
Ku yi murna da matukar farin ciki, domin sakamakonku mai yawan gaske ne a sama. Ta haka ne mutane suka tsananta wa annabawa da suka yi rayuwa kafin ku.
13 You are the salt of the earth, but if the salt may lose savor, in what will it be salted? It is good for nothing from now on, except to be cast outside, and to be trodden down by men.
Ku ne gishirin duniya, amma idan gishiri ya sane yaya za a mai da dandanonsa? Ba zai kara anfani ga komai ba, sai ko a zubar da shi, a tattake a karkashin kafafun mutane.
14 You are the light of the world, a city set on a mountain is not able to be hid;
Ku ne hasken duniya, birnin da ke kan tudu ba shi boyuwa.
15 nor do they light a lamp and put it under the measure, but on the lampstand, and it shines to all those in the house;
Mutane ba za su kunna fitila su sa ta karkashin kwando ba, sai ko a dora ta a mazaunin ta, domin ta ba da haske ga kowa da ke gidan.
16 so let your light shine before men, that they may see your good works, and may glorify your Father who [is] in the heavens.
Bari hasken ku ya haskaka gaban mutane yadda za su ga kyawawan ayyukanku su kuma yabi Ubanku da ke cikin sama.
17 Do not suppose that I came to throw down the Law or the Prophets—I did not come to throw down, but to fulfill;
Kada ku yi tsammanin na zo ne domin in rushe shari'a ko annabawa. Ban zo domin in rushe su ba, amma domin in cika su.
18 for truly I say to you, until the heaven and the earth may pass away, one iota or one tittle may not pass away from the Law, until all may come to pass.
Domin gaskiya ina gaya maku, har sama da kasa su shude, amma digo ko wasali daya ba za ya shude ba a cikin shari'ar, sai an cika dukan al'amura.
19 Therefore whoever may loose one of these commands—the least—and may teach men so, he will be called least in the kingdom of the heavens, but whoever may do and may teach [them], he will be called great in the kingdom of the heavens.
Saboda haka duk wanda ya karya mafi kankanta daga cikin dokokin nan ko kuwa ya koya wa wasu su yi haka, za a kira shi mafi kankanta a cikin mulkin sama. Amma dukan wanda ya kiyaye su ko kuwa ya koyar da su, za a kira shi mafi girma a cikin mulkin sama.
20 For I say to you that if your righteousness may not abound above that of the scribes and Pharisees, you may not enter into the kingdom of the heavens.
Gama ina gaya maku cewa idan adalcin ku bai zarce adalcin marubuta da Farisawa ba, babu yadda za ku shiga mulkin sama.
21 You heard that it was said to the ancients: You will not murder, and whoever may murder will be in danger of the judgment;
Kun ji dai an ce wa mutanen da, 'Kada ka yi kisan kai,' kuma 'Duk wanda ya yi kisan kai yana cikin hatsarin hukunci.'
22 but I say to you that everyone who is angry at his brother without cause will be in danger of the judgment, and whoever may say to his brother, Stupid, will be in danger of the Sanhedrin, and whoever may say, Moron, will be in danger of the Gehenna of fire. (Geenna )
Amma ina gaya muku, duk wanda ya yi fushi da dan'uwansa, yana cikin hatsarin hukunci. Kuma duk wanda ya ce da dan'uwansa, 'Kai mutumin banza!' yana cikin hatsarin tsayawa gaban majalisa, kowa kuma ya ce da dan'uwan sa 'Kai wawa!' yana cikin hatsarin shiga wutar jahannama. (Geenna )
23 If, therefore, you may bring your gift to the altar, and there may remember that your brother has anything against you,
Saboda haka idan za ka yi baiko a bagadi sai ka tuna cewa dan'uwanka yana da damuwa da kai,
24 leave there your gift before the altar, and go—first be reconciled to your brother, and then having come, bring your gift.
ka bar baikon ka a gaban bagadin, ka yi tafiyarka. Da farko dai, ka sasanta da dan'uwanka kafin ka zo ka mika baikon.
25 Be agreeing with your opponent quickly, while you are in the way with him, that the opponent may not deliver you to the judge, and the judge may deliver you to the officer, and you may be cast into prison;
Ka yi sulhu da mai karar ka tun kana hanyar zuwa gaban shari'a, domin kada mai karar ka ya mika ka ga alkali, alkali kuwa ya mika ka ga dogarai, za a kuwa jefa ka a kurkuku.
26 truly I say to you, you may not come forth from there until you may pay the last penny.
Gaskiya ina gaya maka, ba za ka taba fita daga can ba sai ko ka biya dukan kudin da ya ke binka.
27 You heard that it was said to the ancients: You will not commit adultery;
Kun dai ji an ce, 'Kada ka yi zina'.
28 but I say to you that everyone who is looking on a woman to desire her, already committed adultery with her in his heart.
Amma ina gaya maku, duk wanda ya dubi mace, da muguwar sha'awa, ya riga ya yi zina da ita a zuciyarsa.
29 But if your right eye causes you to stumble, pluck it out and cast from you, for it is good to you that one of your members may perish, and not your whole body be cast into Gehenna. (Geenna )
Idan idonka na dama zai sa ka tuntube, kwakule shi ka jefar daga gareka. Don gara daya daga cikin gabobinka ya halaka, da a jefa dukan jikin ka a jahannama. (Geenna )
30 And if your right hand causes you to stumble, cut it off, and cast from you, for it is good to you that one of your members may perish, and not your whole body be cast into Gehenna. (Geenna )
Ko kuwa idan hannunka na dama zai sa ka tuntube, ka yanke shi ka jefar daga gare ka. Domin gara daya daga cikin gabobin ka ya halaka, da a jefa dukan jikinka a jahannama. (Geenna )
31 And it was said that, Whoever may put away his wife, let him give to her a writing of divorce;
An sake fada, 'Duk wanda ya kori matarsa, sai ya ba ta takaddar saki.'
32 but I say to you that whoever may put away his wife, except for the matter of whoredom, makes her to commit adultery; and whoever may marry her who has been put away commits adultery.
Amma ina gaya maku ko wa ya saki matarsa, idan ba a kan laifin lalata ba, ya mai da ita mazinaciya kenan. Kuma duk wanda ya aure ta bayan sakin, ya yi zina kenan.
33 Again, you heard that it was said to the ancients: You will not swear falsely, but you will pay to the LORD your oaths;
Kun sake ji an ce wa wadan da suke a zamanin da, 'Kada ku yi rantsuwar karya, amma ku yi rantsuwar ku ga Ubangiji.'
34 but I say to you not to swear at all; neither by Heaven, because it is the throne of God,
Amma ina gaya maku, kada ku yi rantsuwa sam, ko da sama domin kursuyin Allah ne;
35 nor by the earth, because it is His footstool, nor by Jerusalem, because it is [the] city of [the] great King,
ko kuwa da duniya, domin mazaunin kafafunsa ne, ko da Urushalima, domin birnin babban sarki ne.
36 nor may you swear by your head, because you are not able to make one hair white or black;
Ko ma ace ku yi rantsuwa da kanku, domin ba za ku iya mai da gashin kanku baki ko fari ba.
37 but let your word be, Yes, Yes, No, No, and that which is more than these is of the evil [one].
Amma bari maganarku ta zama 'I, I', ko kuwa 'A'a, a'a.' Duk abin da ya wuce wannan, daga mugun yake.
38 You heard that it was said: Eye for eye, and tooth for tooth;
Kun dai ji an ce, “Ido a maimakon ido, hakori kuma a maimakon hakori.'
39 but I say to you not to resist the evil, but whoever will slap you on your right cheek, turn to him also the other;
Amma ina gaya maku, kada ku yi jayayya da wanda ke mugu, a maimakon haka, ko wa ya mare ku a kuncin dama, ku juya masa dayan ma.
40 and whoever is willing to take you to law, and to take your coat—also permit to him the cloak.
Idan wani yana da niyyar kai kararku gaban shari'a saboda ya karbi rigarku, ku ba wannan mutumin mayafinku ma.
41 And whoever will impress you one mile, go with him two;
Duk wanda ya tilasta ku ga tafiyar mil daya, ku je da shi biyu.
42 to him who is asking of you be giving, and him who is willing to borrow from you, you may not turn away.
Ku ba kowa da ya tambaye ku, kuma kada ku hana kowa da ke neman rance a wurinku.
43 You heard that it was said: You will love your neighbor, and will hate your enemy;
Kun ji abin da aka fada, 'Za ka kaunaci makwabcin ka ka ki magabcin ka.'
44 but I say to you, love your enemies, bless those cursing you, do good to those hating you, and pray for those accusing you falsely, and persecuting you,
Amma ina gaya maku, ku kaunaci magabtan ku, ku yi addu'a domin masu tsananta maku, ku albarkaci wadanda suka la'ance ku, ku yi alheri ga wadanda suke kin ku,
45 that you may be sons of your Father in the heavens, because He causes His sun to rise on evil and good, and He sends rain on righteous and unrighteous.
domin ku zama 'ya'yan Ubanku da ke cikin sama. Domin yakan sa rana ta haskaka wa mugu da mutumin kirki, kuma yakan aiko da ruwan sama ga adali da azzalumi.
46 For if you may love those loving you, what reward do you have? Do the tax collectors not also do the same?
Domin idan kuna kaunar wadanda suke kaunarku, wanne lada kuka samu? Ba haka masu karban haraji ma suke yi ba?
47 And if you may greet your brothers only, what do you do abundant? Do the nations not also do so?
Kuma in kun gaida 'yan'uwanku kadai, me kuke yi fiye da sauran? Ba hakanan al'ummai ma suke yi ba?
48 You will therefore be perfect, as your Father who [is] in the heavens is perfect.”
Saboda haka, lalle ne ku zama cikakku, kamar yadda Ubanku na sama yake cikakke.