< Matthew 27 >

1 And morning having come, all the chief priests and the elders of the people took counsel against Jesus, so as to put Him to death;
Da gari ya waye, duk manyan firistoci da dattawan jama'a suka shirya yadda zasu kulla makirci domin su kashe shi.
2 and having bound Him, they led [Him] away, and delivered Him up to Pontius Pilate, the governor.
Suka daure shi, suka mika shi ga gwamna Bilatus.
3 Then Judas—he who delivered Him up—having seen that He was condemned, having regretted, brought back the thirty pieces of silver to the chief priests and to the elders, saying,
Sa'adda Yahuza, wanda ya bashe shi, ya ga an zartarwa Yesu hukuncin kisa, ya nemi tuba ya kuma mayar da azurfar talatin ga manyan firistocin da dattawan,
4 “I sinned, having delivered up innocent blood”; and they said, “What [is that] to us? You will see!”
yace, “Na yi zunubi ta wurin cin amanar mara laifi.” Amma sukace, “Ina ruwan mu? Ka ji da shi da kanka?”
5 And having cast down the pieces of silver in the temple, he departed, and having gone away, he strangled himself.
Sai ya jefar da kwandalolin azurfar a kasa cikin haikalin ya kuma bar su, ya tafi ya rataye kansa.
6 And the chief priests having taken the pieces of silver, said, “It is not lawful to put them into the treasury, seeing it is the price of blood”;
Sai babban firist ya dauki kwandalolin azurfar ya ce, “Ba daidai bane bisa ga shari'a musa wannan cikin ma'aji, saboda kudin jini ne.”
7 and having taken counsel, they bought the potter’s field with them, for the burial of strangers;
Sai suka tattauna al'amarin a tsakanin su, kudin kuma suka sayi filin maginin tukwane domin makabatar baki.
8 therefore that field was called, “Field of Blood,” to this day.
Dalilin wannan ne ake kiran wurin, “Filin jini” har yau.
9 Then was fulfilled that spoken through Jeremiah the prophet, saying, “And I took the thirty pieces of silver, the price of Him who has been priced, whom they of the sons of Israel priced,
Sai abin da aka fada ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa, “Suka dauki tsabar azurfa talatin na farashin da mutanen Isra'ila suka sa a kansa,
10 and gave them for the potter’s field, as the LORD appointed to me.”
suka bayar domin sayen filin mai tukwane, kamar yadda Ubangiji ya umarce ni.”
11 And Jesus stood before the governor, and the governor questioned Him, saying, “Are You the King of the Jews?” And Jesus said to him, “You say [it].”
Sai Yesu ya tsaya a gaban gwamna, gwamna ya kuma tambaye shi, “Kai sarkin Yahudawa ne?” Yesu ya amsa, “Haka ka fada.”
12 And in His being accused by the chief priests and the elders, He did not answer anything;
Amma da manyan firistocin da dattawan suka zarge shi, bai ce komai ba.
13 then Pilate says to Him, “Do You not hear how many things they witness against You?”
Sai Bilatus yace masa, “Baka ji dukan zarge-zargen da ake yi maka ba?”
14 And He did not answer him, not even to one word, so that the governor wondered greatly.
Amma bai ce masa ko kalma guda ba, sai gwamna yayi matukar mamaki.
15 And at the celebration the governor had been accustomed to release one to the multitude, a prisoner, whom they willed,
To lokacin bikin idi, al'adar gwamna ne ya saki mutum guda wanda jama'a suka zaba.
16 and they had a noted prisoner then, called Barabbas,
A wannan lokacin suna da wani sanannen dan kurkuku mai suna Barabbas.
17 therefore they having been gathered together, Pilate said to them, “Whom do you will [that] I may release to you? Barabbas or Jesus who is called Christ?”
To da suka tattaru, sai Bilatus yace masu, “Wa kuke so a sakar maku? Barabbas, ko Yesu wanda ake kira Almasihu?”
18 For he had known that they had delivered Him up because of envy.
Saboda ya san sun kawo shi ne domin kishi.
19 And as he is sitting on the judgment seat, his wife sent to him, saying, “Nothing—to you and to that Righteous One, for I suffered many things today in a dream because of Him.”
Da yake zaune a kujerar shari'a, matarsa ta aika masa cewa, “Ka fita sha'anin mutumin nan marar laifi. Saboda na sha wahala sosai a yau cikin mafarki saboda shi.”
20 And the chief priests and the elders persuaded the multitudes that they might ask for themselves Barabbas, and might destroy Jesus;
A lokacin nan manyan firistoci da dattawa suka rinjayi ra'ayin jama'a suce a sakar masu da Barabbas, a kashe Yesu.
21 and the governor answering said to them, “Which of the two will you [that] I may release to you?” And they said, “Barabbas.”
Sai gwamna ya tambayesu, “Wa kuke so a sakar maku?” Sukace, “Barabbas.”
22 Pilate says to them, “What then will I do with Jesus who is called Christ?” They all say to him, “Let [Him] be crucified!”
Bilatus yace masu, “Me zan yi da Yesu wanda ake kira Almasihu?” Sai duka suka amsa, “A gicciye shi.”
23 And the governor said, “Why, what evil did He do?” And they were crying out the more, saying, “Let [Him] be crucified!”
Sai yace, “Don me, wane laifi ya aikata?” Amma suka amsa da babbar murya, “A gicciye shi”
24 And Pilate having seen that it profits nothing, but rather a tumult is made, having taken water, he washed the hands before the multitude, saying, “I am innocent from the blood of this Righteous One; you will see [to it] yourselves”;
Amma da Bilatus ya ga ba zai iya komai ba don hargitsi zai iya barkewa, ya dauki ruwa ya wanke hannuwansa a gaban jama'a, yace, “Ba ni da laifi ga jinin mutumin nan marar laifi. Ku yi abin da kuka ga dama.”
25 and all the people answering said, “His blood [is] on us, and on our children!”
Duka mutanen sukace, “Bari jininsa ya kasance a kan mu da 'ya'yan mu.”
26 Then he released Barabbas to them, and having scourged Jesus, he delivered [Him] up that He may be crucified;
Sai ya sakar masu da Barabbas amma yayi wa Yesu bulala ya mika shi garesu domin su gicciye shi.
27 then the soldiers of the governor having taken Jesus to the Praetorium, gathered to Him all the band;
Sai sojojin gwamna suka dauki Yesu zuwa farfajiya suka kuma tara dukan rundunar sojoji.
28 and having unclothed Him, they put a crimson cloak around Him,
Suka yi masa tumbur sa'annan suka sa masa jar alkyabba.
29 and having plaited Him a garland out of thorns they put [it] on His head, and [put] a reed in His right hand, and having kneeled before Him, they were mocking Him, saying, “Hail, the King of the Jews!”
Sai suka yi masa rawanin kaya suka sa a kansa, suka kuma bashi sanda a hannunsa na dama. Suka rusuna a gabansa suna masa ba'a, suna cewa, “Ranka ya dade, Sarkin Yahudawa!”
30 And having spit on Him, they took the reed, and were striking on His head;
Suka kuma tofa masa yawu, suka kwace sandar suka buga masa a ka.
31 and when they had mocked Him, they took off the cloak from Him, and put His own garments on Him, and led Him away to crucify [Him].
Bayan sun gama masa ba'a, suka cire masa alkyabbar suka sa masa kayansa, suka jagorance shi zuwa wurin da za a gicciye shi.
32 And coming forth, they found a man, a Cyrenian, by name Simon: they impressed him that he might carry His cross;
Da suka fito waje, sai suka iske wani Bakurame mai suna Saminu, wanda suka tilasta ya tafi tare dasu domin ya dauki gicciyen.
33 and having come to a place called Golgotha, which is called “Place of [the] Skull,”
Suka iso wani wuri da ake kira Golgotta, wanda ke nufin,”Wurin kwalluwa.”
34 they gave Him vinegar mixed with gall to drink, and having tasted, He would not drink.
Suka bashi ruwan inabi da aka gauraya da wani abu mai daci. Amma da ya 'dan-'dana shi sai ya ki sha.
35 And having crucified Him, they divided His garments, casting a lot, [[that it might be fulfilled which was spoken by the prophet: “They divided My garments to themselves, and they cast a lot over My clothing”; ]]
Bayan da suka gicciye shi, suka kada kuri'a a kan rigarsa.
36 and sitting down, they were watching Him there,
Suka kuma zauna suna kallonsa.
37 and they put up over His head, His accusation written: “THIS IS JESUS, THE KING OF THE JEWS.”
A sama da kansa suka sa abinda ake tuhumarsa da ita a rubuce, “Wannan shine sarkin Yahudawa.”
38 Then two robbers are crucified with Him, one on the right hand and one on the left,
An gicciye shi da 'yanfashi guda biyu, daya ta damansa dayan kuma ta hagunsa.
39 and those passing by kept slandering Him, wagging their heads,
Wadanda suke wucewa suna zaginsa, suna girgiza kai,
40 and saying, “You that are throwing down the temple, and in three days building [it], save Yourself; if You are the Son of God, come down from the cross.”
suna kuma cewa, “Kai da kace zaka rushe haikali ka kuma gina shi a kwana uku, ka ceci kanka mana! In dai kai Dan Allah ne, ka sauko daga gicciyen!”
41 And in like manner also the chief priests mocking, with the scribes and elders, said,
Ta haka ma manyan firistocin suka rika yi masa ba'a, tare da marubuta da shugabannin, suna cewa,
42 “He saved others; He is not able to save Himself! If He is King of Israel, let Him come down now from the cross, and we will believe Him;
“Ya ceci wasu amma ya kasa ceton kansa. Shi ne sarkin Isra'ila. Ya sauko mana daga kan gicciyen, sai mu ba da gaskiya gareshi.
43 He has trusted on God, let Him now deliver Him if He wants Him, because He said, I am [the] Son of God”;
Tun da ya yarda da Allah. Bari Allahn ya cece shi mana, saboda yace, “Ni dan Allah ne.”
44 with the same also the robbers, who were crucified with Him, were reproaching Him.
Hakan nan ma 'yanfashin guda biyu da aka gicciye su tare suka zage shi.
45 And from the sixth hour darkness came over all the land to the ninth hour,
To tun da tsakar rana sai duhu ya rufe kasar gaba daya har karfe uku na yamma.
46 and about the ninth hour Jesus cried out with a great voice, saying, “Eli, Eli, lama sabachthani?” That is, “My God, My God, why did You forsake Me?”
Wajen karfe uku, Yesu ya tada murya mai karfi yace, “Eli, Eli lama sabaktani?” wanda ke nufin, “Allahna, Allahna, don me ka yashe ni?”
47 And certain of those standing there having heard, said, “He calls Elijah”;
Da wadanda suke tsaye kusa suka ji haka, sai sukace, “Yana kiran Iliya.”
48 and immediately, one of them having run, and having taken a sponge, having filled [it] with vinegar, and having put [it] on a reed, was giving Him to drink,
Nan take wani ya ruga da gudu ya dauki soso ya tsoma cikin ruwan inabi mai tsami ya soka kan sandar kara ya mika masa ya sha.
49 but the rest said, “Let alone, let us see if Elijah comes—about to save Him.”
Sai sauran sukace, “Rabu da shi mu gani ko Iliya zai zo ya cece shi.”
50 And Jesus having again cried with a great voice, yielded the spirit;
Sai Yesu ya ta da murya mai karfi yayi kuka sai ya saki ruhunsa.
51 and behold, the veil of the temple was torn in two from top to bottom, and the earth quaked, and the rocks were split,
Sai labullen haikali ya yage gida biyu daga sama zuwa kasa. Kasa kuma ta girgiza, duwatsu suka farfashe.
52 and the tombs were opened, and many bodies of the holy ones who have fallen asleep, arose,
Kaburbura suka bude, tsarkaka kuwa wadanda suke barci da yawa suka tashi.
53 and having come forth out of the tombs after His rising, they went into the holy city, and appeared to many.
Suka fito daga kaburbura bayan tashinsa, suka shiga birni mai tsarki suka bayyana ga mutane da yawa.
54 And the centurion, and those with him watching Jesus, having seen the earthquake, and the things that were done, were exceedingly afraid, saying, “Truly this was God’s Son.”
Da hafsan sojan da wadanda suke kallon Yesu suka ga girgizar kasar da abinda ya faru, suka ji tsoro kwarai sukace, “Hakika wannan Dan Allah ne”
55 And there were there many women beholding from afar, who followed Jesus from Galilee, ministering to Him,
Mata dayawa da suka bi Yesu daga Galili domin su lura da shi suka tsaya suna kallo daga nesa.
56 among whom was Mary the Magdalene, and Mary the mother of James and of Joses, and the mother of the sons of Zebedee.
A cikin su akwai Maryamu Magadaliya, Maryamu uwar Yesu da Yusufu, da uwar 'ya'yan Zabadi.
57 And evening having come, there came a rich man from Arimathea named Joseph, who also himself was discipled to Jesus,
Da yamma sai wani attajiri mutumin Armatiya ya zo, mai suna Yusufu wanda shi ma almajirin Yesu ne.
58 he having gone near to Pilate, asked for himself the body of Jesus; then Pilate commanded the body to be given back.
Ya je wurin Bilatus ya roka a bashi jikin Yesu. Sai Bilatus ya umarta a bashi.
59 And having taken the body, Joseph wrapped it in clean linen,
Yusufu ya dauki jikin, ya rufe shi da likafani mai tsabta,
60 and laid it in his new tomb that he hewed in the rock, and having rolled a great stone to the door of the tomb, he went away;
sai ya sa shi a cikin sabon kabarinsa da ya sassaka cikin dutse. Sai ya mirgina babban dutse a bakin kofar kabarin ya tafi.
61 now Mary the Magdalene was there, and the other Mary, sitting opposite the grave.
Maryamu Magadaliya da dayan Maryamun suna nan zaune akasin kabarin.
62 And on the next day that is after the Preparation, the chief priests and the Pharisees were gathered together to Pilate,
Washegari, wato bayan ranar Shiri, Sai manyan firistoci da Farisawa suka taru tare da Bilatus.
63 saying, “Lord, we have remembered that this deceiver said while yet living, After three days I rise;
Sukace, “Mai gida, mun tuna lokacin da mayaudarin nan yake da rai, yace, “Bayan kwana uku zan tashi.”
64 command, then, the grave to be made secure until the third day, lest His disciples, having come by night, may steal Him away, and may say to the people, He rose from the dead, and the last deceit will be worse than the first.”
Saboda haka, ka bada umarni a tsare kabarin na kwana uku. In ba haka ba almajiransa zasu zo su sace shi, kuma su ce wa mutane, “Ya tashi daga mattatu.” Kuma yaudarar karshe zata fi ta farko muni.”
65 And Pilate said to them, “You have a guard, go away, make [it] secure—as you have known”;
Bilatus yace masu, “Ku dauki masu tsaro. Kuyi tsaro iyakar karfin ku.”
66 and they, having gone, made the grave secure, having sealed the stone, together with the guard.
Sai suka tafi suka tsare kabarin, suka hatimce dutsen, suka sa masu tsaro.

< Matthew 27 >