< Matthew 23 >

1 Then Jesus spoke to the multitudes, and to His disciples,
Sa’an nan Yesu ya ce wa taron mutane da kuma almajiransa,
2 saying, “On the seat of Moses sat down the scribes and the Pharisees;
“Malaman dokoki da Farisiyawa suke zama a kujerar Musa.
3 all, then, as much as they may say to you to observe, observe and do, but according to their works do not do, for they say, and do not do;
Saboda haka dole ku yi musu biyayya, ku kuma yi duk abin da suka faɗa muku. Sai dai kada ku yi abin da suke yi, gama ba sa yin abin da suke wa’azi.
4 for they bind together burdens [too] heavy and grievous to bear, and lay [them] on the shoulders of men, but with their finger they will not move them.
Sukan ɗaura kaya masu nauyi, su sa wa mutane a kafaɗa. Amma su kansu, ba sa ko sa yatsa su taimaka.
5 And all their works they do to be seen by men, and they make broad their phylacteries, and enlarge the fringes of their garments,
“Kome suke yi, suna yi ne don mutane su gani. Sukan yi layunsufantam-fantam bakin rigunarsu kuma sukan kai har ƙasa;
6 they also cherish the first couches at the banquets, and the first seats in the synagogues,
suna son wurin zaman manya a wurin biki, da kuma wuraren zama gaba-gaba a majami’u;
7 and the salutations in the marketplaces, and to be called by men, Rabbi, Rabbi.
suna so a yi ta gaisuwarsu a kasuwa, ana kuma riƙa ce musu, ‘Rabbi.’
8 And you may not be called Rabbi, for one is your teacher—the Christ, and you are all brothers;
“Amma kada a kira ku ‘Rabbi,’ gama kuna da Maigida ɗaya ne, ku duka kuwa,’yan’uwa ne.
9 and you may not call [any] your father on the earth, for one is your Father, who is in the heavens,
Kada kuma ku kira wani a duniya ‘uba,’ gama kuna da Uba ɗaya ne, yana kuwa a sama.
10 nor may you be called teachers, for one is your teacher—the Christ.
Ba kuwa za a kira ku ‘malam’ ba, gama kuna da Malami ɗaya ne, Kiristi.
11 And the greater of you will be your servant,
Mafi girma a cikinku, zai zama bawanku.
12 and whoever will exalt himself will be humbled, and whoever will humble himself will be exalted.
Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi, duk kuma wanda ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.
13 Woe to you, scribes and Pharisees, hypocrites! Because you shut up the kingdom of the heavens before men, for you do not go in, nor do you permit those going in to enter.
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, ku munafukai! Kun rufe ƙofar mulkin sama a gaban mutane. Ku kanku ba ku shiga ba, ba kuwa bar waɗanda suke ƙoƙarin shiga su shiga ba.
14 [[Woe to you, scribes and Pharisees, hypocrites! Because you eat up the houses of the widows, and for a pretense make long prayers, because of this you will receive more abundant judgment.]]
15 Woe to you, scribes and Pharisees, hypocrites! Because you go around the sea and the dry land to make one proselyte, and whenever it may happen—you make him a son of Gehenna twofold more than yourselves. (Geenna g1067)
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan yi tafiye-tafiye zuwa ƙasashe, ku ƙetare teku don ku sami mai tuba ɗaya, sa’ad da ya tuba kuwa, sai ku mai da shi ɗan wuta fiye da ku, har sau biyu. (Geenna g1067)
16 Woe to you, blind guides, who are saying, Whoever may swear by the temple, it is nothing, but whoever may swear by the gold of the temple—is debtor!
“Kaitonku, makafi jagora! Kukan ce, ‘In wani ya rantse da haikali, ba damuwa; amma in ya rantse da zinariyar haikali, sai rantsuwar ta kama shi.’
17 Fools and blind! For which [is] greater, the gold, or the temple that is sanctifying the gold?
Wawaye makafi! Wanne ya fi girma, zinariyar, ko haikalin da yake tsarkake zinariyar?
18 And, Whoever may swear by the altar, it is nothing, but whoever may swear by the gift that is on it—is debtor!
Kukan kuma ce, ‘In wani ya rantse da bagade, ba damuwa; amma in ya rantse da bayarwar da take bisansa, sai rantsuwar ta kama shi.’
19 Fools and blind! For which [is] greater, the gift, or the altar that is sanctifying the gift?
Makafi kawai! Wanne ya fi girma, bayarwar, ko kuwa bagaden da yake tsarkake bayarwar?
20 He therefore who swore by the altar, swears by it, and by all things on it;
Saboda haka, duk wanda ya rantse da bagade, ya rantse ne da bagaden tare da abin da yake bisansa.
21 and he who swore by the temple, swears by it, and by Him who is dwelling in it;
Kuma duk wanda ya rantse da haikali, ya rantse ne da shi da kuma wanda yake zaune a cikinsa.
22 and he who swore by Heaven, swears by the throne of God, and by Him who is sitting on it.
Duk kuma wanda ya rantse da sama, ya rantse ne da kursiyin Allah da kuma wanda yake zaune a kansa.
23 Woe to you, scribes and Pharisees, hypocrites! Because you give tithe of the mint, and the dill, and the cumin, and neglected the weightier things of the Law—judgment, and kindness, and faith; these it was necessary to do, and those not to neglect.
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan ba da kashi ɗaya bisa goma na kayan yajinku, na’ana’a, anise, da lafsur. Amma kun ƙyale abubuwan da suka fi girma na dokoki, adalci, jinƙai da aminci. Waɗannan ne ya kamata da kun kiyaye ba tare da kun ƙyale sauran ba.
24 Blind guides! Who are straining out the gnat, and are swallowing the camel.
Makafi jagora! Kukan tace ƙwaro ɗan mitsil amma sai ku haɗiye raƙumi.
25 Woe to you, scribes and Pharisees, hypocrites! Because you make clean the outside of the cup and the plate, and within they are full of robbery and self-indulgence.
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan wanke bayan kwaf da kwano, amma a ciki, cike suke da zalunci da sonkai.
26 Blind Pharisee! First cleanse the inside of the cup and the plate, that the outside of them may also become clean.
Kai makaho Bafarisiye! Ka fara wanke cikin kwaf da kwano, sa’an nan bayan ma zai zama da tsabta.
27 Woe to you, scribes and Pharisees, hypocrites! Because you are like to whitewashed graves, which outwardly indeed appear beautiful, and within are full of bones of dead men, and of all uncleanness;
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kuna kama da kaburburan da aka shafa musu farin fenti, waɗanda suna da kyan gani a waje, amma a ciki, cike suke da ƙasusuwan matattu da kuma kowane irin abu mai ƙazanta.
28 so also you outwardly indeed appear to men righteous, and within you are full of hypocrisy and lawlessness.
Haka ku ma, a waje, a idon mutane, ku masu adalci ne, amma a ciki, cike kuke da munafunci da mugunta.
29 Woe to you, scribes and Pharisees, hypocrites! Because you build the graves of the prophets, and adorn the tombs of the righteous,
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan gina kaburbura don annabawa, ku kuma yi wa kaburburan mutane masu adalci ado.
30 and say, If we had been in the days of our fathers, we would not have been partakers with them in the blood of the prophets.
Kuna cewa, ‘Da mun kasance a zamanin kakanninmu, ai, da ba mu haɗa hannu da su muka karkashe annabawa ba.’
31 So that you testify to yourselves that you are sons of them who murdered the prophets;
Ta haka kuna ba da shaida a kanku cewa ku zuriyar waɗanda suka karkashe annabawa ne.
32 and you fill up the measure of your fathers.
To, sai ku ci gaba ku cikasa ayyukan da kakanninku suka fara!
33 Serpents! Brood of vipers! How may you escape from the judgment of Gehenna? (Geenna g1067)
“Ku macizai!’Ya’yan macizai! Ta yaya za ku tsere wa hukuncin jahannama ta wuta? (Geenna g1067)
34 Because of this, behold, I send to you prophets, and wise men, and scribes, and of them you will kill and crucify, and of them you will scourge in your synagogues, and will pursue from city to city,
Saboda haka ina aika muku da annabawa, da masu hikima da malamai. Waɗansunsu za ku kashe ku kuma gicciye; waɗansu kuma za ku yi musu bulala a majami’unku kuna kuma binsu gari-gari.
35 that on you may come all the righteous blood being poured out on the earth from the blood of Abel the righteous, to the blood of Zacharias son of Barachias, whom you murdered between the temple and the altar:
Ta haka alhakin jinin masu adalcin da aka zubar a duniya, tun daga jinin Habila mai adalci, zuwa jinin Zakariya ɗan Berekiya, wanda kuka kashe tsakanin haikali da bagade zai koma kanku.
36 truly I say to you, all these things will come on this generation.
Gaskiya nake gaya muku, duk wannan zai auko wa wannan zamani.
37 Jerusalem, Jerusalem, that are killing the prophets, and stoning those sent to you, how often I willed to gather your children together, as a hen gathers her own chickens under the wings, and you did not will.
“Urushalima, ayya Urushalima, ke da kike kashe annabawa, kike kuma jifan waɗanda aka aiko gare ki, sau da sau na so in tattara’ya’yanki wuri ɗaya, yadda kaza takan tattara’ya’yanta cikin fikafikanta, amma kuka ƙi.
38 Behold, your house is left to you desolate;
Ga shi, an bar muku gidanku a yashe.
39 for I say to you, you may not see Me from now on, until you may say, Blessed [is] He who is coming in the Name of the LORD.”
Gama ina gaya muku, ba za ku sāke ganina ba sai kun ce, ‘Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji.’”

< Matthew 23 >